Home General INEC ta buƙaci naira biliyan 126 a kasafin kuɗinta na 2025

INEC ta buƙaci naira biliyan 126 a kasafin kuɗinta na 2025

Hukumar zaɓen Najeriya ta yi buƙaci a ware mata naira biliyan 126 a matsayin kuɗin da za ta kashe a shekarar 2025.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka ranar Juma’a, a lokacin da ya bayyana a gaban kwamitin haɗin gwiwa na majalisar dokokin ƙasar don kare kasafin kuɗin hukumar na 2024.

Tun da farko shugaban hukumar ya yi watsi da naira biliyan 40 da aka ware wa hukumarsa a kasafin kuɗin wannan shekara.

Yana mai danganta hakan da ƙaruwar tsadar abubuwa a Najeriya ciki har da kayayyakin aikin zaɓe.

”Zaɓe a Najeriya ya kasance wani babban abu da ke buƙatar wadatattun kuɗi, don haka abin da muke buƙata a wannan shekara ya kai naira biliyan 126, kuma muna da takardun da ke ɗauke da cikakkun bayanan yadda za mu kashe waɗannan kuɗaɗe da muka buƙata”, in ji Farfesa Yakubu.

Daga cikin ayyukan da ya ce hukumar za ta gudanar a shekarar sun haɗa da cigaba da aikin rajistar masu zaɓe, da shirya zaɓukan wasu jihohin a bana, da sauya wasu kayyakin zaɓen da suka lalace da gyara ofisoshin hukumar da ke wasu ƙanann hukumomi.

Haka kuma ya ce shekarar 2025, shekara ce mai muhimmanci ga hukumar wajen shirya zaɓukan 2027.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp