Home General INEC ta buƙaci naira biliyan 126 a kasafin kuɗinta na 2025

INEC ta buƙaci naira biliyan 126 a kasafin kuɗinta na 2025

Hukumar zaɓen Najeriya ta yi buƙaci a ware mata naira biliyan 126 a matsayin kuɗin da za ta kashe a shekarar 2025.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka ranar Juma’a, a lokacin da ya bayyana a gaban kwamitin haɗin gwiwa na majalisar dokokin ƙasar don kare kasafin kuɗin hukumar na 2024.

Tun da farko shugaban hukumar ya yi watsi da naira biliyan 40 da aka ware wa hukumarsa a kasafin kuɗin wannan shekara.

Yana mai danganta hakan da ƙaruwar tsadar abubuwa a Najeriya ciki har da kayayyakin aikin zaɓe.

”Zaɓe a Najeriya ya kasance wani babban abu da ke buƙatar wadatattun kuɗi, don haka abin da muke buƙata a wannan shekara ya kai naira biliyan 126, kuma muna da takardun da ke ɗauke da cikakkun bayanan yadda za mu kashe waɗannan kuɗaɗe da muka buƙata”, in ji Farfesa Yakubu.

Daga cikin ayyukan da ya ce hukumar za ta gudanar a shekarar sun haɗa da cigaba da aikin rajistar masu zaɓe, da shirya zaɓukan wasu jihohin a bana, da sauya wasu kayyakin zaɓen da suka lalace da gyara ofisoshin hukumar da ke wasu ƙanann hukumomi.

Haka kuma ya ce shekarar 2025, shekara ce mai muhimmanci ga hukumar wajen shirya zaɓukan 2027.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp