Home General INEC ta buƙaci naira biliyan 126 a kasafin kuɗinta na 2025

INEC ta buƙaci naira biliyan 126 a kasafin kuɗinta na 2025

Hukumar zaɓen Najeriya ta yi buƙaci a ware mata naira biliyan 126 a matsayin kuɗin da za ta kashe a shekarar 2025.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka ranar Juma’a, a lokacin da ya bayyana a gaban kwamitin haɗin gwiwa na majalisar dokokin ƙasar don kare kasafin kuɗin hukumar na 2024.

Tun da farko shugaban hukumar ya yi watsi da naira biliyan 40 da aka ware wa hukumarsa a kasafin kuɗin wannan shekara.

Yana mai danganta hakan da ƙaruwar tsadar abubuwa a Najeriya ciki har da kayayyakin aikin zaɓe.

”Zaɓe a Najeriya ya kasance wani babban abu da ke buƙatar wadatattun kuɗi, don haka abin da muke buƙata a wannan shekara ya kai naira biliyan 126, kuma muna da takardun da ke ɗauke da cikakkun bayanan yadda za mu kashe waɗannan kuɗaɗe da muka buƙata”, in ji Farfesa Yakubu.

Daga cikin ayyukan da ya ce hukumar za ta gudanar a shekarar sun haɗa da cigaba da aikin rajistar masu zaɓe, da shirya zaɓukan wasu jihohin a bana, da sauya wasu kayyakin zaɓen da suka lalace da gyara ofisoshin hukumar da ke wasu ƙanann hukumomi.

Haka kuma ya ce shekarar 2025, shekara ce mai muhimmanci ga hukumar wajen shirya zaɓukan 2027.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp