Home General Gwamna Yusuf ya biya biliyan 16 ga yan fansho a Kano

Gwamna Yusuf ya biya biliyan 16 ga yan fansho a Kano

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya jaddada kudirin gwamnatinsa na cigaba da biyan yan fansho hakkokinsu domin inganta jin dadi da walwalarsu.

” Gwamnatinmu ta damu da walwalarku shi yasa tun da na zo nake cigaba da biyan wadanda suka kammala aiki hakkokinsu, wanda a yau na kaddamar da kashi na uku na biyanku kudaden gama Aiki wato Gratuity”.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa PRNigeria.

Ya ce daga daga hawan gwamnan Yusuf Kan karagar mulki ya biya kimanin naira Biliyan 16 ga yan fansho wanda ya ce hakan zai kara inganta jin dadi da walwalarsu da ma cigaban tattalin arzikin jihar Kano.

” Karon farko na ware biliyan 6 domin biyan wadanda suka gama aiki daga matakin albashi na 10 zuwa kasa, yayin da a kashi na biyu muka biya biliyan 5 ga wadanda suka kammala aiki sakamakon cika shekaru 35″. Inji Abba Kabir

Sanarwar ta kara da cewa gwamna Yusuf ya yi alkawarin cigaba da biyan yan fansho hakkokinsu, inda yace bai dace a bar su haka ba, idan aka yi la’akari da irin gudunmawar da suka bayar don cigaban jihar Kano a lokacin da suke aiki.

Ya ce zai cigaba da biyan yan fansho hakkokinsu ba tare da bata lokaci ba, inda ya ba su tabbacin za kuma a cigaba da biyansu kudinsu na wata-wata ba tare da wata matsala ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp