Home General Gwamna Yusuf ya biya biliyan 16 ga yan fansho a Kano

Gwamna Yusuf ya biya biliyan 16 ga yan fansho a Kano

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya jaddada kudirin gwamnatinsa na cigaba da biyan yan fansho hakkokinsu domin inganta jin dadi da walwalarsu.

” Gwamnatinmu ta damu da walwalarku shi yasa tun da na zo nake cigaba da biyan wadanda suka kammala aiki hakkokinsu, wanda a yau na kaddamar da kashi na uku na biyanku kudaden gama Aiki wato Gratuity”.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa PRNigeria.

Ya ce daga daga hawan gwamnan Yusuf Kan karagar mulki ya biya kimanin naira Biliyan 16 ga yan fansho wanda ya ce hakan zai kara inganta jin dadi da walwalarsu da ma cigaban tattalin arzikin jihar Kano.

” Karon farko na ware biliyan 6 domin biyan wadanda suka gama aiki daga matakin albashi na 10 zuwa kasa, yayin da a kashi na biyu muka biya biliyan 5 ga wadanda suka kammala aiki sakamakon cika shekaru 35″. Inji Abba Kabir

Sanarwar ta kara da cewa gwamna Yusuf ya yi alkawarin cigaba da biyan yan fansho hakkokinsu, inda yace bai dace a bar su haka ba, idan aka yi la’akari da irin gudunmawar da suka bayar don cigaban jihar Kano a lokacin da suke aiki.

Ya ce zai cigaba da biyan yan fansho hakkokinsu ba tare da bata lokaci ba, inda ya ba su tabbacin za kuma a cigaba da biyansu kudinsu na wata-wata ba tare da wata matsala ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp