Home General Kotun daukaka kara a Abuja ta yanke hukunci kan dambarwar Masarautar Kano

Kotun daukaka kara a Abuja ta yanke hukunci kan dambarwar Masarautar Kano

Kotun daukaka kara dake zaman ta a Abuja ta yanke hukuncin cewa babbar kotun tarayya ba ta da hurumin saurarar duk wata kara da ta shafi dokar masarautu.

Haka zalika kotun ta ce sashi na 251 na kundin tsarin mulkin Nijeriya ya yayi bayani dalla-dalla kan harancin kotun tarayya ta shiga al’amarin da ya shafi masarautu.

Kotun tace tsohon sarkin na kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya gaza gabatar da hujjojin da za su gasgata da’awarsa na cewa an tauye masa hakkinsa matsayin sa na dan Adam.

Idan za a iya tunawa Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero bayan da gwamnatin Kano ta ayyana cire shi, ya garzaya gaban babbar kotun tarayya dake Kano domin kalubalantar matakin gwamnatin.

Aminu Ado Bayero yana da’awar cewa an take masa hakkinsa a matsayinsa na dan adam, don haka yake neman kotun da duba labarin, sai dai gwamnatin Kano ta ce kotun tarayyar bata da hurumin saurarar kara lamarin da yasa ta tafi kotun daukaka kara domin nemo fassara.

Kotun daukaka Karar ta ce Babbar kotun tarayyar ba ta da hurumin kamar yadda kotun koli ta Kasa ta taba yanke hukuncin akan shari’ar Tukur da gwamnan gongola.

Kotun ta ce kotun da ke da hurumin shari’ar masarautu a tsarin mulkin Nijeriya, ita ce babbar kotun jiha ba babbar kotun tarayya ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDD
X whatsapp