Home General Tinubu zai tafi taron ɗorewar tattalin arziki a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa

Tinubu zai tafi taron ɗorewar tattalin arziki a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa

Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai tafi ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa domin halartar taron ɗorewar tattalin arziki na duniya ta 2025 (ADSW 2025).

Shugaban ƙasar, Sheikh Mohamed bin Zayed Al Nahyan ne ya gayyaci shugaba Tinubu domin halartar taron – wanda zai gudana tsakanin 12 zuwa 18 ga watan Janairu.

Taron – wanda zai samu halartar manyan shugabannin duniya, da masana da ƙungiyoyin fararen hula da ‘yan kasuwa da masu ruwa da tsaki – zai tattauna nasarorin da aka samu a fannin tattalin arziki da zamantakewa, tare da lalubo hanyoyin ɗorewar ci gaban da aka samu.

Cikin sanarwar bulaguron da fadar shugaban Najeriya ta fitar, ta ce a taron Shugaba Tinubu zai jaddada manufofin gwamnatinsa, ciki har ci gaban tattalin arziki da makamashi da sufuri da fannin lafiya.

Haka kuma tawagar Najeriya a taron za ta gana da fadar sarkin ƙasar domin tattauna batutuwan da suka shafi ƙasashen biyu.

Ministan harkokin wajen ƙasar, Ambassador Yusuf Tuggar na daga cikin manyan jami’an gwamnatin da za su yi wa shugaban rakiya a taron, a cewar sanarwar.

Ana sa ran shugaban zai koma Najeriya bayan kammala taron ranar 16 ga watan Janairu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp