Home General Kotu a Najeriya ta yi watsi da sabbin bukatun da Godwin Emefiele...

Kotu a Najeriya ta yi watsi da sabbin bukatun da Godwin Emefiele ya gabatar mata

Kotun hukunta manyan laifuka da ke jihar Legas a Najeriya, ta yi watsi da bukatar da tsohon gwamnan babban bankin kasara, Godwin Emefiele, ya shigar, yana kalubalantar hukuncin da wata kotu ta yanke bisa zargin badakalar dala biliyan 4.5 da kuma naira biliyan 2.8 da hukumar EFCC ta shigar a kansa.

Mai shari’a Rahman Oshodi, a hukuncin da ya yanke, ya ce kotu na da hurumin gurfanar da Emefiele da wanda ake tuhuma, Henry Omoile.

Sai dai alkalin kotun ya yi fatali da tuhume-tuhume hudu daga cikin tuhume-tuhume 26 da EFCC ta shigar a kan su.

Hukumar EFCC ta gurfanar da Emefiele ne a gaban kuliya bisa tuhume-tuhume 26, da suka shafi karkatar da kudaden da suka kai dala biliyan 4.5 ba bisa ka’ida ba da kuma Naira biliyan 2.8.

A ranar 12 ga Disamba, 2024, lauyan Emefiele, Mista Olalekan Ojo mai mukamin SAN, ya bayar da hujjar cewa kotun ba ta da hurumin sauraren karar a Legas.

Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta dakatar da Emefiele a matsayin gwamnan CBN a ranar 14 ga Yuni, 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Manyan Tsofaffin Jami'an Soji 10 da Suka Rasa Rayukansu a Hannun ƴan Ta'addaTarihin Rayuwar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaMatsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar AbujaDuk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da 'Yan Ta'adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda - Christopher MusaFarashin ɗanyen Mai ya Faɗi Bayan Amurka ta Soke Sabbin Hare-Haren kaiwa IranAmurka ta yi sulhu kan yaƙin da ta ke yi da Iran - TrumpMajalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan JihaHukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar NejaMiyagun ƙwayoyi da Makamai: Jami'an Tsaro Sun Kama Mutane 8 a Jihar YobeAbin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a Sokoto
X whatsapp