Home General Kotu a Najeriya ta yi watsi da sabbin bukatun da Godwin Emefiele...

Kotu a Najeriya ta yi watsi da sabbin bukatun da Godwin Emefiele ya gabatar mata

Kotun hukunta manyan laifuka da ke jihar Legas a Najeriya, ta yi watsi da bukatar da tsohon gwamnan babban bankin kasara, Godwin Emefiele, ya shigar, yana kalubalantar hukuncin da wata kotu ta yanke bisa zargin badakalar dala biliyan 4.5 da kuma naira biliyan 2.8 da hukumar EFCC ta shigar a kansa.

Mai shari’a Rahman Oshodi, a hukuncin da ya yanke, ya ce kotu na da hurumin gurfanar da Emefiele da wanda ake tuhuma, Henry Omoile.

Sai dai alkalin kotun ya yi fatali da tuhume-tuhume hudu daga cikin tuhume-tuhume 26 da EFCC ta shigar a kan su.

Hukumar EFCC ta gurfanar da Emefiele ne a gaban kuliya bisa tuhume-tuhume 26, da suka shafi karkatar da kudaden da suka kai dala biliyan 4.5 ba bisa ka’ida ba da kuma Naira biliyan 2.8.

A ranar 12 ga Disamba, 2024, lauyan Emefiele, Mista Olalekan Ojo mai mukamin SAN, ya bayar da hujjar cewa kotun ba ta da hurumin sauraren karar a Legas.

Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta dakatar da Emefiele a matsayin gwamnan CBN a ranar 14 ga Yuni, 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar ShekaraShugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 
X whatsapp