Home General Za mu yi bincike kan harin jirgin da ya ‘kashe’ ƴan sintiri...

Za mu yi bincike kan harin jirgin da ya ‘kashe’ ƴan sintiri a Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin saman Najeriya ta ce tana gudanar da bincike kan wasu rahotannin da suka ce an kashe fararen hula a yayin wani harin da aka kai a jihar Zamfara da ke yankin arewa maso yammacin ƙasar a karshen makon da ya gabata.

Wata sanarwa da ta fito daga ofishin darektan sashen hulɗa da jama’a da yaɗa labarai na rundunar, Air Vice Marshal Olusola Akinboyewa, ta ce an kai harin ne kan wasu ƴan bindiga a yankin Tungar Kara da ke ƙaramar hukumar Zurmi a jihar ta Zamfara inda aka yi nasarar kuɓutar da wasu da aka yi garkuwa da su.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, duk da ya ke harin ya yi nasarar tarwatsa wani sansanin ƴanbindiga da suka addabi yankin, rundunar ta nuna matuƙar damuwa kan rahotannin rashin rayukan fararen hula da aka samu inda ta ƙara da cewa tana kan gudanar da bincike kuma za a sanar da sakamakon hakan da zaran ya kammala.

Ta kuma bayar da tabbacin cewa zata ci gaba da ɗaukar matakai da za su tabbatar da cewa an kiyaye rayukan fararen hula a yayin da ta ke ƙokarin tabbatar da ingantaccen tsaro a sassan ƙasar.

A ranar Lahadin da ta gabata ne dai mazauna yankin na Tungar Kara suka ce aƙalla mutane 15 ne suka mutu sakamakon harin sojoin, ciki ma har da ƴan sintirin da ke ƙoƙarin yaƙar ƴanbindigan.

A cikin watan Disamba aƙalla mutane 10 ne suka mutu a lokacin da wani jirgin yaƙin soji ya kai hari bisa kuskure kan wasu fararen hula a jihar Sokoto da ke yankin arewa maso yammacin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp