Home General Za mu yi bincike kan harin jirgin da ya ‘kashe’ ƴan sintiri...

Za mu yi bincike kan harin jirgin da ya ‘kashe’ ƴan sintiri a Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin saman Najeriya ta ce tana gudanar da bincike kan wasu rahotannin da suka ce an kashe fararen hula a yayin wani harin da aka kai a jihar Zamfara da ke yankin arewa maso yammacin ƙasar a karshen makon da ya gabata.

Wata sanarwa da ta fito daga ofishin darektan sashen hulɗa da jama’a da yaɗa labarai na rundunar, Air Vice Marshal Olusola Akinboyewa, ta ce an kai harin ne kan wasu ƴan bindiga a yankin Tungar Kara da ke ƙaramar hukumar Zurmi a jihar ta Zamfara inda aka yi nasarar kuɓutar da wasu da aka yi garkuwa da su.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, duk da ya ke harin ya yi nasarar tarwatsa wani sansanin ƴanbindiga da suka addabi yankin, rundunar ta nuna matuƙar damuwa kan rahotannin rashin rayukan fararen hula da aka samu inda ta ƙara da cewa tana kan gudanar da bincike kuma za a sanar da sakamakon hakan da zaran ya kammala.

Ta kuma bayar da tabbacin cewa zata ci gaba da ɗaukar matakai da za su tabbatar da cewa an kiyaye rayukan fararen hula a yayin da ta ke ƙokarin tabbatar da ingantaccen tsaro a sassan ƙasar.

A ranar Lahadin da ta gabata ne dai mazauna yankin na Tungar Kara suka ce aƙalla mutane 15 ne suka mutu sakamakon harin sojoin, ciki ma har da ƴan sintirin da ke ƙoƙarin yaƙar ƴanbindigan.

A cikin watan Disamba aƙalla mutane 10 ne suka mutu a lokacin da wani jirgin yaƙin soji ya kai hari bisa kuskure kan wasu fararen hula a jihar Sokoto da ke yankin arewa maso yammacin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp