Home General Rikicin shugabanci ya janyo zanga-zanga a ofishin jam’iyyar PDP

Rikicin shugabanci ya janyo zanga-zanga a ofishin jam’iyyar PDP

Gomman masu zanga-zanga sun yi dafifi a shelkwatar jam’iyyar PDP ta ƙasa da ke Abuja domin nuna rashin amincewa da kama aikin sabon sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sunday Ude-Okoye wanda kotun ɗaukaka ƙara ta ayyana a matsayin sakataren jam’iyyar, kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Bayanai sun nuna cewa shelkwatar jam’iyyar ta tafi hutun ƙarshen shekara ne a watan Disamba inda kuma a ranar Litinin ake sa ran komawa aiki ranar da sabon sakataren zai kama aiki.

To sai dai masu zanga-zanga da ke goyon bayan senator Sam Anyanwu wanda ake taƙaddama a kansa sun mamaye ƙofar ofishin inda suke ta ihun cewa ” ofishin sakataren jam’iyyar PDP na ƙasa akwai mai shi kuma senator Anyanwu ne sakataren.”

A baya-bayan nan ne dai kotun ɗaukaka ƙara ta Enugu ce ta ayyana cewa Sunday Ude-Okoye ne sakataren jam’iyyar halastacce.

An jibge jami’an tsaro a ƙofar shelkwatar jam’iyyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp