Home General Rikicin shugabanci ya janyo zanga-zanga a ofishin jam’iyyar PDP

Rikicin shugabanci ya janyo zanga-zanga a ofishin jam’iyyar PDP

Gomman masu zanga-zanga sun yi dafifi a shelkwatar jam’iyyar PDP ta ƙasa da ke Abuja domin nuna rashin amincewa da kama aikin sabon sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sunday Ude-Okoye wanda kotun ɗaukaka ƙara ta ayyana a matsayin sakataren jam’iyyar, kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Bayanai sun nuna cewa shelkwatar jam’iyyar ta tafi hutun ƙarshen shekara ne a watan Disamba inda kuma a ranar Litinin ake sa ran komawa aiki ranar da sabon sakataren zai kama aiki.

To sai dai masu zanga-zanga da ke goyon bayan senator Sam Anyanwu wanda ake taƙaddama a kansa sun mamaye ƙofar ofishin inda suke ta ihun cewa ” ofishin sakataren jam’iyyar PDP na ƙasa akwai mai shi kuma senator Anyanwu ne sakataren.”

A baya-bayan nan ne dai kotun ɗaukaka ƙara ta Enugu ce ta ayyana cewa Sunday Ude-Okoye ne sakataren jam’iyyar halastacce.

An jibge jami’an tsaro a ƙofar shelkwatar jam’iyyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp