Home AFIRKA Mayaƙan JNIM da ‘yan tawayen FLA sun ƙaddamar da hari kan tawagar...

Mayaƙan JNIM da ‘yan tawayen FLA sun ƙaddamar da hari kan tawagar sojin Mali

Rundunar sojin Mali ta bayyana cewa, wasu da ake zargi masu iƙirarin jihadi ne tare da haɗin gwiwar ‘yan tawayen FLA, sun ƙaddamar da wani mummunan hari akan wata tawagar sojojin ƙasar a ranar Litinin ɗinnan da ta gabata, a yankin arewacin ƙasar. Sai dai rundunar bata ba da cikakken bayani kan yadda lamarin ya kasance ba.

Bayanai sun nuna cewa bayan da maharan suka kammala aika-aikar tasu a Kidal da safiyar ranar Litinin ɗin, sai suka zarce yankin Anefis domin aiwatar da wata manufar tasu.

Sannan yan tawayen FLA suka bayyana cewa wannan harin sun iske motoci guda hudu a wurin, ciki har da mota mai sulke guda daya, a yayin da suka yi ikirarin cewa sun kwashesu tare da ikirarin cewa sun yi sanadin sanadin mutuwar mutane da dama.

Rundunar sojin Mali a cikin wata sanarwa da ta fitar a wannan Litinin, ta ce an yi arangama, amma ba tare da ba da cikakken bayani kan taho mu gamar da suka yi ba.

Sai dai ‘yan tawayen na FLA sun ba da wata sanarwa akan harin da jirgi mara matuƙi ya kai musu a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp