Home AFIRKA Mayaƙan JNIM da ‘yan tawayen FLA sun ƙaddamar da hari kan tawagar...

Mayaƙan JNIM da ‘yan tawayen FLA sun ƙaddamar da hari kan tawagar sojin Mali

Rundunar sojin Mali ta bayyana cewa, wasu da ake zargi masu iƙirarin jihadi ne tare da haɗin gwiwar ‘yan tawayen FLA, sun ƙaddamar da wani mummunan hari akan wata tawagar sojojin ƙasar a ranar Litinin ɗinnan da ta gabata, a yankin arewacin ƙasar. Sai dai rundunar bata ba da cikakken bayani kan yadda lamarin ya kasance ba.

Bayanai sun nuna cewa bayan da maharan suka kammala aika-aikar tasu a Kidal da safiyar ranar Litinin ɗin, sai suka zarce yankin Anefis domin aiwatar da wata manufar tasu.

Sannan yan tawayen FLA suka bayyana cewa wannan harin sun iske motoci guda hudu a wurin, ciki har da mota mai sulke guda daya, a yayin da suka yi ikirarin cewa sun kwashesu tare da ikirarin cewa sun yi sanadin sanadin mutuwar mutane da dama.

Rundunar sojin Mali a cikin wata sanarwa da ta fitar a wannan Litinin, ta ce an yi arangama, amma ba tare da ba da cikakken bayani kan taho mu gamar da suka yi ba.

Sai dai ‘yan tawayen na FLA sun ba da wata sanarwa akan harin da jirgi mara matuƙi ya kai musu a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp