Home AFIRKA Mayaƙan JNIM da ‘yan tawayen FLA sun ƙaddamar da hari kan tawagar...

Mayaƙan JNIM da ‘yan tawayen FLA sun ƙaddamar da hari kan tawagar sojin Mali

Rundunar sojin Mali ta bayyana cewa, wasu da ake zargi masu iƙirarin jihadi ne tare da haɗin gwiwar ‘yan tawayen FLA, sun ƙaddamar da wani mummunan hari akan wata tawagar sojojin ƙasar a ranar Litinin ɗinnan da ta gabata, a yankin arewacin ƙasar. Sai dai rundunar bata ba da cikakken bayani kan yadda lamarin ya kasance ba.

Bayanai sun nuna cewa bayan da maharan suka kammala aika-aikar tasu a Kidal da safiyar ranar Litinin ɗin, sai suka zarce yankin Anefis domin aiwatar da wata manufar tasu.

Sannan yan tawayen FLA suka bayyana cewa wannan harin sun iske motoci guda hudu a wurin, ciki har da mota mai sulke guda daya, a yayin da suka yi ikirarin cewa sun kwashesu tare da ikirarin cewa sun yi sanadin sanadin mutuwar mutane da dama.

Rundunar sojin Mali a cikin wata sanarwa da ta fitar a wannan Litinin, ta ce an yi arangama, amma ba tare da ba da cikakken bayani kan taho mu gamar da suka yi ba.

Sai dai ‘yan tawayen na FLA sun ba da wata sanarwa akan harin da jirgi mara matuƙi ya kai musu a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp