Home AFIRKA Burkina Faso ta amince da dokar haramta neman maza a faɗin ƙasar

Burkina Faso ta amince da dokar haramta neman maza a faɗin ƙasar

Gwamnatin sojin Burkina Faso ta amince da wata doka da ke haramta neman maza ko luwaɗi a fadin ƙasar, wadda ta tanadi hukuncin ɗaurin shekaru 5 a gidan kaso, lamarin da ya sa ta kasance ƙasar Afirka ta baya-bayan nan da ta samar da wannan doka.

Ƙasashe kimanin 30 a nahiyar Afirka sun haramta ɗabi’ar neman maza, amma Burkina Faso ba ta yi hakan ba gabanin ƙwace mulkin da sojoji suka yi shekaru 3 da suka wuce.

Mambobin majalisar dokokin wucin-gadi da sojoji suka kafa guda 71 ne suka amince da ƙudirin dokar, da aka gabatar.

A jawabin da ya gabatar wa al’ummar ƙasar ta kafar talabijin, ministan shari’a na ƙasar, Edasso Rodrigue Bayala ya ce duk wanda aka kama yana aikata neman maza zai gurfana a gaban alƙali, inda ya ƙara da cewa idan kuma ba dan ƙasa ba ne, za a tasa ƙeyarsa zuwa ƙasarsa.

Dokar na daga cikin dokokin da aka bijiro da su a ƙasar da zummar sake fasalin iyali da tsarin zamantakewar ‘yan ƙasa, kuma za a sanar da al’umma wannan doka ta wajen gudanar da gangami a faɗin ƙasar.

Mali, wadda aminiyar Burkina Faso ce, ta yi wannan doka  da ke haramta luwaɗi a watan Nuwamban shekarar 2024.

Ghana da Uganda sun tsaurara dokokinsu da ke yaƙi da ɗabi’ar neman maza a cikin shekarun baya-bayan nan, lamarin da ya janyo caccaka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp