Home AFIRKA Burkina Faso ta amince da dokar haramta neman maza a faɗin ƙasar

Burkina Faso ta amince da dokar haramta neman maza a faɗin ƙasar

Gwamnatin sojin Burkina Faso ta amince da wata doka da ke haramta neman maza ko luwaɗi a fadin ƙasar, wadda ta tanadi hukuncin ɗaurin shekaru 5 a gidan kaso, lamarin da ya sa ta kasance ƙasar Afirka ta baya-bayan nan da ta samar da wannan doka.

Ƙasashe kimanin 30 a nahiyar Afirka sun haramta ɗabi’ar neman maza, amma Burkina Faso ba ta yi hakan ba gabanin ƙwace mulkin da sojoji suka yi shekaru 3 da suka wuce.

Mambobin majalisar dokokin wucin-gadi da sojoji suka kafa guda 71 ne suka amince da ƙudirin dokar, da aka gabatar.

A jawabin da ya gabatar wa al’ummar ƙasar ta kafar talabijin, ministan shari’a na ƙasar, Edasso Rodrigue Bayala ya ce duk wanda aka kama yana aikata neman maza zai gurfana a gaban alƙali, inda ya ƙara da cewa idan kuma ba dan ƙasa ba ne, za a tasa ƙeyarsa zuwa ƙasarsa.

Dokar na daga cikin dokokin da aka bijiro da su a ƙasar da zummar sake fasalin iyali da tsarin zamantakewar ‘yan ƙasa, kuma za a sanar da al’umma wannan doka ta wajen gudanar da gangami a faɗin ƙasar.

Mali, wadda aminiyar Burkina Faso ce, ta yi wannan doka  da ke haramta luwaɗi a watan Nuwamban shekarar 2024.

Ghana da Uganda sun tsaurara dokokinsu da ke yaƙi da ɗabi’ar neman maza a cikin shekarun baya-bayan nan, lamarin da ya janyo caccaka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp