Home General Kofa ya sanar da ficewarsa da ga NNPP

Kofa ya sanar da ficewarsa da ga NNPP

Dan Majalisa Mai wakiltar kananan hukumomin Kiru/Bebeji a zauren majalisar wakilan Nijeriya Abdulmumin Jibril Kofa ya sanar ficewarsa daga Jam’iyyar NNPP.

ta cikin wata sanarwa da jaridar Politics Digest ta samu kofa ya dangwarar da shahadar Jam’iyyar ne bayan abinda ya kira sharin adalci da shugabancinta yayi masa.

Wannan dai na zuwa ne biyo bayan ikirarin jam’iyyar na korar sa daga cikinta bisa abinda ta kira karya dokokinta tare da gaza biyanta wasu kudade da ya kamata ya biya na hakkoki.

daga cikin abubuwan da Jam’iyyar ta yi wukar kugu da su na korar Kofa akwai wata hira da ya yi a ‘yan tsakaninnan da yake yabon shugaban kasa Tinubu wanda ba Dan Jam’iyyar sa bane, wanda ta ce hakan ya saba dokokinta.

Sai dai kuma Kofa ta cikin sanarwar ficewarsa daga Jam’iyyar yace matakin da Jam’iyyar ta dauka akan sa ya zo masa a matsayin ba zata, kasancewar yasan bai karya wata dokar Jam’iyya.

“ganawar da nayi da manema labarai cikin harshen hausa da turanci, ban fadi wasu kalamai da ya kamata jam’iyyar ta yi min wannan mummunan hukunci ba,” yace hasalima kalamansa sun bi sahun dokoki da tsarin jam’iyyar ya tanadar wanda yake kara dabbaka damar fadin ALbarkacin baka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp