Home General ‘Yan sandan Jigawa sun kama Dilolin kwaya a jihar

‘Yan sandan Jigawa sun kama Dilolin kwaya a jihar

Rundunar ƴan sanda Jihar Jigawa ta samu nasarar cafke mutane 13 da ta ke zargi da dillancin miyagun ƙwayoyi a jihar dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Wannan dai na cikin wata sanarwa da Kakakin rundunar SP Shiisu Lawan Adam, ya fitar wadda ta ce dakarun rundunar sun gudanar da wani sumame a sassan jihar  daga ranar 2 zuwa 6 ga watan satumbar 2025, wanda aka shirya shi bayan samun wasu bayanan sirrin da hukumar ta yi kan masu safarar miyagun ƙwayoyi da wasu masu  tayar da hankulan jama’ar jihar.

Sanarwa ta kara da cewa dakarun suna gudanar da sumamen ne a sassana jihar da suka hadar da Dutse, Guri, Birnin Kudu, Bamaina, Babura da Roni, kan maɓoyar masu laifin da wuraren da suke gudanar da safarar miyagun ƙwayoyin, inda aka kama mutane 13 waɗanda suka haɗa da Basiru Garba, Ladan Muhammad, Hassan Ali, Abubakar Sa’adu, Ahmad Muhammad, Aminu Hamisu, Muhammad Abdullahi, Suleiman Abdullahi, Abubakar Auwalu, Faruk Abdullahi, Isah Ismail, Hassan Aliyu, da Usman Muhammad – dukkaninsu daga sassa daban-daban na Jigawa da Nguru, Jihar Yobe.

A yayin samamen, jami’an ƴan sandan sun ƙwato miyagun ƙwayoyi iri-iri ciki har da Exol guda (704), Tramadol (264), Diazepam (3), D5 (2,042), roba mai wari (48), tabar wiwi (4 blocks da 148 wraps), wayar Vivo (da ake zargin ta sata ce), farare da jajayen kafso (602), da wasu kayan maye sanfurin ruwa har lita 6.

Sanarwar ta ce an miƙa waɗanda ake zargi zuwa kotu bayan kammala cikakken bincike.

Kwamishinan ƴan sandan Jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ya gargaɗi duk masu aikata miyagun laifuka da su daina ko kuma su fuskanci hukuncin doka, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da bayanai masu inganci domin taimakawa rundunar wajen dakile aikata laifi.

Sanarwar ta ƙare da tabbatarwa jama’a cewa rundunar ƴan sanda na ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da zaman lafiya, tsaro da kwanciyar hankali a dukkan ƙananan hukumomin jihar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp