Home AFIRKA Shugabannin sojin Afrika sun kammala taron tsaro a Abuja

Shugabannin sojin Afrika sun kammala taron tsaro a Abuja

Shugabannin sojin Afrika sun kammala wani taro na ƙoli a Abuja wanda ya mayar da hankali kan yawaitar matsalolin tsaro a nahiyar.

Shugabannin tsaro daga ƙasashe irin su Nijar da Somaliya da Ghana da Masar sun hallara a babban birnin Najeriya domin tattaunawa kan dabarun zaman lafiya da tsaro na cikin gida.

An kammala wannan taro mai tsawon kwanaki uku a ranar Laraba.

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ne ya yi jawabi ga mahalarta a lokacin buɗe taron, inda ya buƙaci kasashen Afrika su zama masu fito da sabbin fasahohi a fannin tsaro, tare da gargadin cewa dogaro da hanyoyin waje ba zai dore ba.

Haka kuma, ya jaddada buƙatar ƙara zuba jari a tsaron shafukan sada zumunta da na intanet, ganin yadda barazanar da ba a gani da kuma ta zamani ke karuwa.

Nahiyar na ci gaba da fuskantar matsaloli kamar ta’addanci da laifukan ƙungiyoyi da fashi da makami da hare-hare ƴan bindiga da tasirin sauyin yanayi.

Kungiyar Tarayyar Afrika da ECOWAS sun dage wajen karfafa hadin gwiwar soja, amma hakan ya ci tura sakamakon ƙarancin kuɗaɗe da matsalolin kayan aiki da sabanin siyasa.

Daya daga cikin muhimman batutuwa a taron shi ne kafa Rundunar Tsaron ko-ta-kwana ta Afrika wadda aka daɗe ana shirin kafa ta domin amsa kiran gaggawa, amma aiwatar da ita ya tsaya sakamakon matsaloli wajen dabaru da ƙa’idoji da kuɗade.

Mahalarta sun amince cewa Afrika dole ta samar da sabon tsarin tsaro – wanda ‘yan Afrika za su jagoranta kuma su tsara shi domin magance matsalolin nahiyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp