Home AFIRKA Shugabannin sojin Afrika sun kammala taron tsaro a Abuja

Shugabannin sojin Afrika sun kammala taron tsaro a Abuja

Christopher-Musa

Shugabannin sojin Afrika sun kammala wani taro na ƙoli a Abuja wanda ya mayar da hankali kan yawaitar matsalolin tsaro a nahiyar.

Shugabannin tsaro daga ƙasashe irin su Nijar da Somaliya da Ghana da Masar sun hallara a babban birnin Najeriya domin tattaunawa kan dabarun zaman lafiya da tsaro na cikin gida.

An kammala wannan taro mai tsawon kwanaki uku a ranar Laraba.

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ne ya yi jawabi ga mahalarta a lokacin buɗe taron, inda ya buƙaci kasashen Afrika su zama masu fito da sabbin fasahohi a fannin tsaro, tare da gargadin cewa dogaro da hanyoyin waje ba zai dore ba.

Haka kuma, ya jaddada buƙatar ƙara zuba jari a tsaron shafukan sada zumunta da na intanet, ganin yadda barazanar da ba a gani da kuma ta zamani ke karuwa.

Nahiyar na ci gaba da fuskantar matsaloli kamar ta’addanci da laifukan ƙungiyoyi da fashi da makami da hare-hare ƴan bindiga da tasirin sauyin yanayi.

Kungiyar Tarayyar Afrika da ECOWAS sun dage wajen karfafa hadin gwiwar soja, amma hakan ya ci tura sakamakon ƙarancin kuɗaɗe da matsalolin kayan aiki da sabanin siyasa.

Daya daga cikin muhimman batutuwa a taron shi ne kafa Rundunar Tsaron ko-ta-kwana ta Afrika wadda aka daɗe ana shirin kafa ta domin amsa kiran gaggawa, amma aiwatar da ita ya tsaya sakamakon matsaloli wajen dabaru da ƙa’idoji da kuɗade.

Mahalarta sun amince cewa Afrika dole ta samar da sabon tsarin tsaro – wanda ‘yan Afrika za su jagoranta kuma su tsara shi domin magance matsalolin nahiyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp