Home AFIRKA Shugabannin sojin Afrika sun kammala taron tsaro a Abuja

Shugabannin sojin Afrika sun kammala taron tsaro a Abuja

Christopher-Musa

Shugabannin sojin Afrika sun kammala wani taro na ƙoli a Abuja wanda ya mayar da hankali kan yawaitar matsalolin tsaro a nahiyar.

Shugabannin tsaro daga ƙasashe irin su Nijar da Somaliya da Ghana da Masar sun hallara a babban birnin Najeriya domin tattaunawa kan dabarun zaman lafiya da tsaro na cikin gida.

An kammala wannan taro mai tsawon kwanaki uku a ranar Laraba.

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ne ya yi jawabi ga mahalarta a lokacin buɗe taron, inda ya buƙaci kasashen Afrika su zama masu fito da sabbin fasahohi a fannin tsaro, tare da gargadin cewa dogaro da hanyoyin waje ba zai dore ba.

Haka kuma, ya jaddada buƙatar ƙara zuba jari a tsaron shafukan sada zumunta da na intanet, ganin yadda barazanar da ba a gani da kuma ta zamani ke karuwa.

Nahiyar na ci gaba da fuskantar matsaloli kamar ta’addanci da laifukan ƙungiyoyi da fashi da makami da hare-hare ƴan bindiga da tasirin sauyin yanayi.

Kungiyar Tarayyar Afrika da ECOWAS sun dage wajen karfafa hadin gwiwar soja, amma hakan ya ci tura sakamakon ƙarancin kuɗaɗe da matsalolin kayan aiki da sabanin siyasa.

Daya daga cikin muhimman batutuwa a taron shi ne kafa Rundunar Tsaron ko-ta-kwana ta Afrika wadda aka daɗe ana shirin kafa ta domin amsa kiran gaggawa, amma aiwatar da ita ya tsaya sakamakon matsaloli wajen dabaru da ƙa’idoji da kuɗade.

Mahalarta sun amince cewa Afrika dole ta samar da sabon tsarin tsaro – wanda ‘yan Afrika za su jagoranta kuma su tsara shi domin magance matsalolin nahiyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp