Home Labarai Gwamnatin tarayya ta dauki matakan dakile sake yajin aikin ASUU a Nijeriya

Gwamnatin tarayya ta dauki matakan dakile sake yajin aikin ASUU a Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Jaddada Aniyarta na Kawo Karshen Matsalolin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU)

Ministan  ilimi Dakta Tuni Al’ada ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai a birnin Abuja, inda ya ce shugaban ƙasa Bila Tinubu yana gudanar da wasu sauye-sauye, domin samun mafita ga kalubalen da ake fuskanta tsakanin kungiyar da Gwamnatin tarayya

Dakta Alausa ya ce, gwamnati ta shiga tattaunawa kai tsaye da ASUU, inda kwamitin da Yayale Ahmed ke jagoranta ya mika shawarwari, kuma an gudanar da taron manyan jami’an gwamnati domin nazari a kai.

Ministan ya bayyana cewa an kafa kwamitin kwararru bakwai karkashin Jagorancin Sakatare Janar na Ma’aikatar Ilimi, domin daidaita matsayar gwamnati kan shawarwarin da aka gabatar.

Ya jaddada cewa gwamnatin Tinubu ba za ta rattaba hannu kan yarjejeniyar da ba za ta iya aiwatarwa ba, ko ta daure Najeriya da igiyar zato.

Ministan ya kuma ce gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da ganin cewa ba a sake samun taƙaddama da ASUU ba, tare da tabbatar da cewa daliban Najeriya suna ci gaba da karatu ba tare da barazanar Yajin Aiki ba.

Ba dai wannan ne karon farko da kungiyar ASUUta yi yunkurin tsunduma yakin aiki a Nijeriyar ba sakamakon abin da take kira rashin cika mata alƙawarin da Gwamnatin tarayya ta zaga cikawa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp