Home Labarai Mun kama tabar wiwi ta naira miliyan 48.5 a Kaduna – Custom

Mun kama tabar wiwi ta naira miliyan 48.5 a Kaduna – Custom

Hukumar Kwastam ta Najeriya ta bayyana cewa jami’anta sun kama tabar wiwi mai darajar naira miliyan 48.5 da wasu kayan da aka haramta na naira miliyan 220 a Jihar Kaduna kamar yadda Gidan talabijin na Channels ya ruwaito.

Kwamandan hukumar ya ce an kama kayayyakin ne a ayyuka daban-daban da aka gudanar ranar 21 ga Agusta, 2025.

Ya ce jami’an sashen bisa ingattatun bayanan da suka samu ne suka tsayar da mota a Zaria kan babbar hanyar zuwa Kano inda suka yi nasarar kama tabar wiwi ɗin da sauran kayan da aka haramta.

Mai magana da yawun hukumar kwastam ya ce an miƙa wanda ake zargin da kayan ga jami’an hukumar yaki da ƙwayoyi ta Nigeria (NDLEA) don ci gaba da bincike da gurfanarwa a gaban shari’a bisa tsarin haɗin gwiwar hukumomi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp