Home AFIRKA Shugabannin ƙasashen Benin da Senegal sun gana don farfaɗo da alaƙarsu

Shugabannin ƙasashen Benin da Senegal sun gana don farfaɗo da alaƙarsu

Shugaban ƙasar Senegal Bassirou Diomaye Faye ya kai wata ziyarar aiki na yini guda ƙasar Benin da yammacin jiya Talata, da nufin ƙarfafa dangantaka da farfaɗo da haɗin gwiwa tsakanin Benin da Senegal.

Shugaba Patrice Talon ya nuna farin cikinsa da wannan ziyarar, musamman da tazo kwanaki kaɗan gabanin bikin tunawa da ranar ƴancin ƙan ƙasar.

Anasa ɓangaren Bassirou Diomaye Faye ya bayyana goyon bayan ƙasarsa ga yaƙin da Benin ke yi da ƴan ta’adda, tare da fatan ƙasashen biyu za su samu ci gaba mai ɗorewa a fannin kasuwanci.

Dangane da Ƙungiyar raya tattalin arziƙin ƙasashen yammacin Afrika ECOWAS kuwa, Faye ya tunanar da shugaba Talon irin ƙalubalen da ƙungiyar ke fuskanta, acewarsa dole ne kamar UEMOA, sai an kawo sauye – sauye domin tunkarar halin da ake ciki yanzu haka.

Wannan dai ita ce ziyarar farko da wani shugaban ƙasar Senegal ya kai Cotonou tun bayan da Patrice Talon ya hau kan karagar mulki a shekarar 2016.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp