Home AFIRKA Shugabannin ƙasashen Benin da Senegal sun gana don farfaɗo da alaƙarsu

Shugabannin ƙasashen Benin da Senegal sun gana don farfaɗo da alaƙarsu

Shugaban ƙasar Senegal Bassirou Diomaye Faye ya kai wata ziyarar aiki na yini guda ƙasar Benin da yammacin jiya Talata, da nufin ƙarfafa dangantaka da farfaɗo da haɗin gwiwa tsakanin Benin da Senegal.

Shugaba Patrice Talon ya nuna farin cikinsa da wannan ziyarar, musamman da tazo kwanaki kaɗan gabanin bikin tunawa da ranar ƴancin ƙan ƙasar.

Anasa ɓangaren Bassirou Diomaye Faye ya bayyana goyon bayan ƙasarsa ga yaƙin da Benin ke yi da ƴan ta’adda, tare da fatan ƙasashen biyu za su samu ci gaba mai ɗorewa a fannin kasuwanci.

Dangane da Ƙungiyar raya tattalin arziƙin ƙasashen yammacin Afrika ECOWAS kuwa, Faye ya tunanar da shugaba Talon irin ƙalubalen da ƙungiyar ke fuskanta, acewarsa dole ne kamar UEMOA, sai an kawo sauye – sauye domin tunkarar halin da ake ciki yanzu haka.

Wannan dai ita ce ziyarar farko da wani shugaban ƙasar Senegal ya kai Cotonou tun bayan da Patrice Talon ya hau kan karagar mulki a shekarar 2016.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp