Home AFIRKA Zanga-zanga ta barke a sansanin ƴan gudun hijra mafi girma da ke...

Zanga-zanga ta barke a sansanin ƴan gudun hijra mafi girma da ke Kenya

Wasu Rahotannin sun bayyana cewa zanga-zanga ta ɓarke a daya daga cikin manyan sansanonin ‘yan gudun hijira na Kenya a ranar Litinin, inda aka samu rahoton mutuwar mutum ɗaya da jikkatar wasu, bayan watanni da aka shafe ana tankiya saboda katsewar agaji.

Sansanin ‘yan gudun hijira na Kakuma, da ke arewacin Kenya, shine na biyu mafi girma a ƙasar, kuma yana ɗaukar ‘yan gudun hijira kusan 300,000 daga Sudan ta Kudu da Somalia da Uganda da kuma Burundi.

Ƙungiyoyin agaji sun sha fama da tankiya tsawon watanni bayan katse tallafin da Amurka da sauran masu ba da agaji suka yi.

Wata majiya daga ma’aikatar kula da ‘yan gudun hijira ta shaida wa kamfanin dillacin labarai na AFP cewa, Mutum ɗaya ya mutu, kuma wasu jami’an ‘yan sanda biyu sun jikkata, yana mai cewa an samu karuwar matsin lamba kan tsarin tallafin.

Duk da haka, kakakin ‘yan sanda ƙasar Michael Muchiri ya tabbatar da kasancewar jami’an a wajen rikicin amma ya ce babu wanda ya rasa ransa.

Ya ce matakin da gwamnatin Amurka ta ɗauka na katse tallafin USAID ya fara yin tasiri a kan halin da ‘yan gudun hijira ke ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp