Home AFIRKA Zanga-zanga ta barke a sansanin ƴan gudun hijra mafi girma da ke...

Zanga-zanga ta barke a sansanin ƴan gudun hijra mafi girma da ke Kenya

Wasu Rahotannin sun bayyana cewa zanga-zanga ta ɓarke a daya daga cikin manyan sansanonin ‘yan gudun hijira na Kenya a ranar Litinin, inda aka samu rahoton mutuwar mutum ɗaya da jikkatar wasu, bayan watanni da aka shafe ana tankiya saboda katsewar agaji.

Sansanin ‘yan gudun hijira na Kakuma, da ke arewacin Kenya, shine na biyu mafi girma a ƙasar, kuma yana ɗaukar ‘yan gudun hijira kusan 300,000 daga Sudan ta Kudu da Somalia da Uganda da kuma Burundi.

Ƙungiyoyin agaji sun sha fama da tankiya tsawon watanni bayan katse tallafin da Amurka da sauran masu ba da agaji suka yi.

Wata majiya daga ma’aikatar kula da ‘yan gudun hijira ta shaida wa kamfanin dillacin labarai na AFP cewa, Mutum ɗaya ya mutu, kuma wasu jami’an ‘yan sanda biyu sun jikkata, yana mai cewa an samu karuwar matsin lamba kan tsarin tallafin.

Duk da haka, kakakin ‘yan sanda ƙasar Michael Muchiri ya tabbatar da kasancewar jami’an a wajen rikicin amma ya ce babu wanda ya rasa ransa.

Ya ce matakin da gwamnatin Amurka ta ɗauka na katse tallafin USAID ya fara yin tasiri a kan halin da ‘yan gudun hijira ke ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp