Home AFIRKA Zanga-zanga ta barke a sansanin ƴan gudun hijra mafi girma da ke...

Zanga-zanga ta barke a sansanin ƴan gudun hijra mafi girma da ke Kenya

Wasu Rahotannin sun bayyana cewa zanga-zanga ta ɓarke a daya daga cikin manyan sansanonin ‘yan gudun hijira na Kenya a ranar Litinin, inda aka samu rahoton mutuwar mutum ɗaya da jikkatar wasu, bayan watanni da aka shafe ana tankiya saboda katsewar agaji.

Sansanin ‘yan gudun hijira na Kakuma, da ke arewacin Kenya, shine na biyu mafi girma a ƙasar, kuma yana ɗaukar ‘yan gudun hijira kusan 300,000 daga Sudan ta Kudu da Somalia da Uganda da kuma Burundi.

Ƙungiyoyin agaji sun sha fama da tankiya tsawon watanni bayan katse tallafin da Amurka da sauran masu ba da agaji suka yi.

Wata majiya daga ma’aikatar kula da ‘yan gudun hijira ta shaida wa kamfanin dillacin labarai na AFP cewa, Mutum ɗaya ya mutu, kuma wasu jami’an ‘yan sanda biyu sun jikkata, yana mai cewa an samu karuwar matsin lamba kan tsarin tallafin.

Duk da haka, kakakin ‘yan sanda ƙasar Michael Muchiri ya tabbatar da kasancewar jami’an a wajen rikicin amma ya ce babu wanda ya rasa ransa.

Ya ce matakin da gwamnatin Amurka ta ɗauka na katse tallafin USAID ya fara yin tasiri a kan halin da ‘yan gudun hijira ke ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp