Home General Hadarin jirgin ruwa yayi sanadin mutuwar mutum 6 a jihar Jigawa

Hadarin jirgin ruwa yayi sanadin mutuwar mutum 6 a jihar Jigawa

Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa a Arewa Maso yammacin Nijeriya ta tabbatar da mutuwar mutane 7 cikin su har da kananan yara sakamakon hadarin jirgin ruwa a karamar hukumar Taura dake jihar.

Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin rundunar SP Shi’isu Lawan Adam, Anipr, ya aikewa PRNigeria a yammacin ranar talata, inda ya ce  rundunar ta nuna bakin cikin ta bisa aukuwar hadarin da ya rutsa da matafiya a kauyen Zangwan Maje dake karamar hukumar ta Taura.

Sanarwa ta ce a ranar 27 ga watan Yunin 2025, rundunar ta sami wani kiran gaggawa da ke cewa a kalla yara 15 dake kan hanyarsu ta dawowa daga gona a Jejin Gunka zuwa kauyen Zangwan Maje jirgin da suke ciki ya kife bisa Ambaliyar ruwa da iska mai karfi da kuma lodin da suka yiwa jirgin ya wuce kima.

Sai dai bayan daukin gaggawa da aka kai musu an sami nasarar kubutar da yara 7 a raye, yayin da aka sami nasarar gano gawarwakin yara 2 dukkanninsu mata, haka nan kuma a safiyar talata an sami nasarar gano gawarwakin yara mata 4.

Tuni dai likitoci suka tabbatar da mutuwar yaran kamar yadda sanarwar ta tabbatar.

Kwamishinan ‘yansandan jihar CP, Dahiru Muhammad, psc, fdc ya mika ta’aziyyarsa ga iyalai da ‘yan uwan wadanda hadarin ya rutsa da su da ma daukacin al’ummar kauyen Zangwan Maje.

Ya kuma yi kira ga mazauna yankin da su kaucewa yin tafiyar dare, tare da gujewa daukar kayan da suka wuce kima, su kuma ringumi yin amfani da rigar ruwa a dukkan lokacin da za su shiga jirgin ruwa.

Daga PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp