Home General Hadarin jirgin ruwa yayi sanadin mutuwar mutum 6 a jihar Jigawa

Hadarin jirgin ruwa yayi sanadin mutuwar mutum 6 a jihar Jigawa

Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa a Arewa Maso yammacin Nijeriya ta tabbatar da mutuwar mutane 7 cikin su har da kananan yara sakamakon hadarin jirgin ruwa a karamar hukumar Taura dake jihar.

Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin rundunar SP Shi’isu Lawan Adam, Anipr, ya aikewa PRNigeria a yammacin ranar talata, inda ya ce  rundunar ta nuna bakin cikin ta bisa aukuwar hadarin da ya rutsa da matafiya a kauyen Zangwan Maje dake karamar hukumar ta Taura.

Sanarwa ta ce a ranar 27 ga watan Yunin 2025, rundunar ta sami wani kiran gaggawa da ke cewa a kalla yara 15 dake kan hanyarsu ta dawowa daga gona a Jejin Gunka zuwa kauyen Zangwan Maje jirgin da suke ciki ya kife bisa Ambaliyar ruwa da iska mai karfi da kuma lodin da suka yiwa jirgin ya wuce kima.

Sai dai bayan daukin gaggawa da aka kai musu an sami nasarar kubutar da yara 7 a raye, yayin da aka sami nasarar gano gawarwakin yara 2 dukkanninsu mata, haka nan kuma a safiyar talata an sami nasarar gano gawarwakin yara mata 4.

Tuni dai likitoci suka tabbatar da mutuwar yaran kamar yadda sanarwar ta tabbatar.

Kwamishinan ‘yansandan jihar CP, Dahiru Muhammad, psc, fdc ya mika ta’aziyyarsa ga iyalai da ‘yan uwan wadanda hadarin ya rutsa da su da ma daukacin al’ummar kauyen Zangwan Maje.

Ya kuma yi kira ga mazauna yankin da su kaucewa yin tafiyar dare, tare da gujewa daukar kayan da suka wuce kima, su kuma ringumi yin amfani da rigar ruwa a dukkan lokacin da za su shiga jirgin ruwa.

Daga PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp