Home Labarai An samu raguwar hare-haren Boko Haram da na ƴan bindiga – Ribadu

An samu raguwar hare-haren Boko Haram da na ƴan bindiga – Ribadu

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya ce an samu raguwar hare-haren Boko Haram da na ƴanbindiga har ma da rikice-rikice tsakanin al’ummomi a yankin arewacin ƙasar cikin shekaru biyu da suka wuce karkashin gwamnatin shugaba Tinubu – idan aka kwatanta da gwamnatin da ta gabata.

Ya bayar da misalin cewa an kashe mutum 1,192 sannan an sace sama da 3,348 a jihar Kaduna a gwamnatin da ta shuɗe, yayin da sama da mutane 5,000 suka rasa rayukansu a jihar Benue a wannan lokaci.

Ribadu ya bayyana haka ne a yau Talata yayin jawabi a taron masu ruwa da tsaki na arewacin Najeriya wanda aka gudanar a jihar Kaduna.

Ya ce nasarar da aka samu a yaƙi da rashin tsaro ya samo asali ne sakamakon umarnin da shugaba Tinubu ya bai wa jami’an tsaro kan bin tsarin tabbatar da tsaro na bai-ɗaya.

Ya ƙara da cewa an samu nasarar sakin mutum 11,259 waɗanda aka yi garkuwa da su a watan Mayu kaɗai – a wasu samame daban-daban da sojojin Najeriya suka kai a arewa maso yamma.

Ribadu ya kuma bayyana cewa jami’an tsaro sun kashe shugabannin ƴanbindiga da mambobinsu da dama a jihohin Zamfara da Kaduna da kuma Katsina.

Mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan tsaro ya yaba wa gwamnan jihar Kaduna Uba Sani kan amfani da hanyoyi daban-daban wajen shawo kan matsalar tsaro a kudancin jihar da Birnin Gwari har ma da wasu yankuna da ke fama da matsalar tsaro a faɗin jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp