Home Labarai zamu hallaka Da;iban da ke hannun mu matukar baku biya Fansa ba...

zamu hallaka Da;iban da ke hannun mu matukar baku biya Fansa ba – ‘Yan Bindiga

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun ƙwarewar a aikin lauya da aka sace a jihar Benue sun ce idan ba a biya kuɗin fansa ba, za su kashe su.

An sace ɗaliban ne a ranar 26 ga watan Yulin a hanyarsu ta zuwa makarantar domin samun horo da ke Yola a jihar Adamawa da ke arewa maso gabashin ƙasar daga jihar Anambra da ke kudu maso gabashi.

jaridar ta Punch ta ruwaito daga wata majiya cewa masu garkuwar sun ƙara kuɗin fansar daga dala 13,110 zuwa dala 32,688 kan kowane ɗalibi, sannan suka yi barazanar kashe ɗaliban matuƙar ba a biya kuɗin ba.

“Sun ce idan ba mu kawo kuɗin ba, za su kashe su, sanan sun gargaɗe mu kada mu saka jami’an tsaro a maganar.”

Kakakin runduar ƴansandan jihar Adamawa, Yahaya Suleiman ya ce suna aiki tare da rundunar jihar Benuwai domin ceto ɗaliban.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp