Home Labarai zamu hallaka Da;iban da ke hannun mu matukar baku biya Fansa ba...

zamu hallaka Da;iban da ke hannun mu matukar baku biya Fansa ba – ‘Yan Bindiga

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun ƙwarewar a aikin lauya da aka sace a jihar Benue sun ce idan ba a biya kuɗin fansa ba, za su kashe su.

An sace ɗaliban ne a ranar 26 ga watan Yulin a hanyarsu ta zuwa makarantar domin samun horo da ke Yola a jihar Adamawa da ke arewa maso gabashin ƙasar daga jihar Anambra da ke kudu maso gabashi.

jaridar ta Punch ta ruwaito daga wata majiya cewa masu garkuwar sun ƙara kuɗin fansar daga dala 13,110 zuwa dala 32,688 kan kowane ɗalibi, sannan suka yi barazanar kashe ɗaliban matuƙar ba a biya kuɗin ba.

“Sun ce idan ba mu kawo kuɗin ba, za su kashe su, sanan sun gargaɗe mu kada mu saka jami’an tsaro a maganar.”

Kakakin runduar ƴansandan jihar Adamawa, Yahaya Suleiman ya ce suna aiki tare da rundunar jihar Benuwai domin ceto ɗaliban.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp