Home Labarai Gwamnan Zamfara ya Amince da Nadin Sabon Sarki Gusau

Gwamnan Zamfara ya Amince da Nadin Sabon Sarki Gusau

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da nadin Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello a matsayin Sarki na 16 na Masarautar Gusau, wanda ya gaji mahaifinsa, Marigayi Dr. Ibrahim Bello, da ya rasu a ranar 25 ga Yuli bayan shekaru goma yana sarauta.

Nadin ya biyo bayan shawarwarin masu zaben sarki na masarautar Gusau, tare da bin al’adun gargajiya da dokoki na kasa.

Alhaji Abdulkadir, wanda shi ne babban ɗan marigayi sarki, yana rike da sarautar Bunun Gusau kafin wannan nadin. Shi ɗan asalin Malam Sambo Dan Ashafa ne.

Gwamna Dauda Lawal ya taya sabon sarki murna tare da kira gare shi da ya ci gaba da gadon kyakkyawar rayuwa da dabi’un sarakunan da suka gabata, wanda zai zama jigo wajen ɗorewar zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba a masarautar Gusau da ma kewaye

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp