Home Labarai Kotu da dakatar da ƙungiyar Likitoci masu neman ƙwarewa daga shiga yajin...

Kotu da dakatar da ƙungiyar Likitoci masu neman ƙwarewa daga shiga yajin aiki

Kotun ƙwadago a Najeriya ta dakatar da shirin ƙungiyar likitoci masu neman ƙwarewa ta ƙasar na tsunduma yajin aikin sai baba ta gani da suka tsara farawa daga ranar 12 ga watan da muke na Janairun.

Kotun ƙwadagon ta Najeriyar ƙarƙashin mai shari’a Justice Emmanuel Subilim a jiya Juma’a ta umarci shugaban ƙungiyar ta NARD Dr Mohammad Usman Suleiman da sakataren ƙungiyar Dr Shu’aibu Ibrahim da su dakatar da aniyar tsunduma yajin aikin.

Tun farko gwamnatin Najeriya ƙarƙashin ofishin ministan shari’a ne ta garzaya kotun don dakatar da likitocin daga faro wannan yajin aiki da ta ce zai kassara harkokin kulawar lafiya.

Cikin takardar da ke ɗauke da umarnin kotun, Mai shari’a Subilim ya haramtawa ƙungiyar duk wani shirin bore ko ƙauracewa aiki ta kowacce fuska, har zuwa lokacin da za a ci gaba da sauraren shari’ar a ranar 21 ga watan nan.

Kafin wannan hukunci tarin asibitoci a sassan Najeriya ciki har da na koyarwa sun fara amsa kiran uwar ƙungiyar ta NARD wajen faro yajin aikin a ranar Litinin mai zuwa.

Sanarwar NARD da tun farko ta buƙaci tafiya yajin aikin ɗauke da sa hannun shugabanta Dr Suleiman ta ce an cimma matsayar tsunduma yajin aiki na sai baba ta gani ne yayin babban taron ƙungiyar na ranar 2 ga watan nan sakamakon gaza samun daidaito tsakaninsu da gwamnatin Najeriya kan jerin buƙatunsu na haƙƙoki da aka gaza biyansu dama alƙawuran da gwamnatin ƙasar ta gaza cika musu.

Wannan yajin aiki da suka yiwa ta ke da “Ba aiwatarwa ba komawa bakin aiki” ana ganin zai kasance mafi tsanani da ƙungiyar ta taɓa idan har da ta yi nasarar faro shi ganin cewa likitocin ba za su koma bakin aiki ba har sai an aiwatar da dukkanin buƙatunsu.

Tsawon lokaci aka shafe ana kai ruwa rana tsakanin gwamnatin Najeriya da ƙungiyoyin ma’aikatan ɓangaren lafiya kama daga Likitocin da takwarorinsu malaman jinya lamarin da kan kai ga yajin aiki a lokuta dama.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp