Home Labarai ICPC za ta ci gaba da binciken shugaban NMDPRA duk da Dangote...

ICPC za ta ci gaba da binciken shugaban NMDPRA duk da Dangote ya janye ƙorafinsa

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ICPC ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da gudanar da bincike kan tsohon shugaban hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Najeriya, (NMDPRA), Farouk Ahmed, duk da cewa attajiri mafi kuɗi a Afirka, Alhaji Aliko Dangote ya janye ƙorafin da ya shigar a kansa.

Lauyan Dangote, Ogwu Onoja, ne ya aika takardar janye ƙorafin zuwa ga ICPC.

Dangote dai ya buƙaci hukumar ta binciki Ahmed a watan Disamban 2025 kan zargin amfani da muƙaminsa wajen satar kuɗaɗen gwamnati, inda ya ce yana da hujjoji da suka tabbatar da zarginsa.

Sai dai, mai magana da yawun ICPC, John Odey, ya bayyana cewa duk da janyewar ƙorafin, hukumar za ta ci gaba da bincike domin tabbatar da gaskiya da adalci da kuma yaƙi da cin hanci a Najeriya.

Odey ya ƙara da cewa ci gaba da binciken zai nuna cewa hukumar na yin aikinta ba tare da la’akari da matsayi ko shaharar mutum ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp