Home General Tinubu zai yi hadin Gwiwa da Abba Gida Gida don samar da...

Tinubu zai yi hadin Gwiwa da Abba Gida Gida don samar da wutar Lantarki

Gwamnatin tarayya Nijeriya na shirin yin hadin gwiwa da Gwamnatin Kano, don samar da tashar wutar lantarki mai zaman kanta a jihar dake arewacin kasar.

Ministan makamashi na kasa Chief Adebayo Adelabu ne ya bayyana hakan a yayin wata ziyara da ya kai jihar a yammacin ranar Alhamis, inda yace wannan kudiri zai taimaka matuka wajen kaucewa matsalolin wutar lantarki a jihar dake matsayin cibiyar kasuwanci a yankin da kuma kaucewa sake lalacewar wutar da ya jefa da dama cikin halin kakanakayi.

Wannan na zuwa ne bayan da aka kwashe tsahon kwanaki a yankin babu wutar ta lantarki, lamarin da ya shafi jihohi 17, abin da ya jefa al’ummar cikin duhu da asara mai yawa a fannin kasuwancin.

Hukumomi sun yi zargin cewa ‘yanbindiga ne suka tunkuɗe layin wutar da ke kai wa arewa maso yamma, da arewa maso gabas, da wani ɓangare na arewa ta tsakiya wutar.

Da yake jawabi a lokacin da ya tarbi ministan Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir yusuf wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan fadar Gwamantin Kano, Mal. Shehu wada Sagagi, ya nuna damuwar sa matuka kan halin da A’ummar jihar Kano suka shiga bisa daukewar wutar lantakin.

“daukewar wutar lantarkin nan ya saka al’ummar mu cikin mawuyacin hali wanda ya haifar da asarar mai dumbin yawa”

Ya kuma bukaci gwamnatin tarayya ta duba yiwuwar biyan diyya ga wadanda wannan lamarin ya shafa.

Da yake jawabi a yayin ziyarar ministan Manajan daraktan kamfanin rarraba wutar ta nan jahar Kano KEDCO Abubakar Yusuf, ya tabbatarwa da al’ummar Kano cewa kamfanin KEDCO ya shirya tsaf dan ganin an Samu wuta wadacciya a fadin jahohin Kano da Katsina da Jigawa.

Ministan ya ziyarci gidan rarraba wuta na Kumbotso da tashar wuta mai amfani da hasken rana ta zawaciki wato Bagaja Renewable Energy Company.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp