Home General Tinubu zai yi hadin Gwiwa da Abba Gida Gida don samar da...

Tinubu zai yi hadin Gwiwa da Abba Gida Gida don samar da wutar Lantarki

Gwamnatin tarayya Nijeriya na shirin yin hadin gwiwa da Gwamnatin Kano, don samar da tashar wutar lantarki mai zaman kanta a jihar dake arewacin kasar.

Ministan makamashi na kasa Chief Adebayo Adelabu ne ya bayyana hakan a yayin wata ziyara da ya kai jihar a yammacin ranar Alhamis, inda yace wannan kudiri zai taimaka matuka wajen kaucewa matsalolin wutar lantarki a jihar dake matsayin cibiyar kasuwanci a yankin da kuma kaucewa sake lalacewar wutar da ya jefa da dama cikin halin kakanakayi.

Wannan na zuwa ne bayan da aka kwashe tsahon kwanaki a yankin babu wutar ta lantarki, lamarin da ya shafi jihohi 17, abin da ya jefa al’ummar cikin duhu da asara mai yawa a fannin kasuwancin.

Hukumomi sun yi zargin cewa ‘yanbindiga ne suka tunkuɗe layin wutar da ke kai wa arewa maso yamma, da arewa maso gabas, da wani ɓangare na arewa ta tsakiya wutar.

Da yake jawabi a lokacin da ya tarbi ministan Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir yusuf wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan fadar Gwamantin Kano, Mal. Shehu wada Sagagi, ya nuna damuwar sa matuka kan halin da A’ummar jihar Kano suka shiga bisa daukewar wutar lantakin.

“daukewar wutar lantarkin nan ya saka al’ummar mu cikin mawuyacin hali wanda ya haifar da asarar mai dumbin yawa”

Ya kuma bukaci gwamnatin tarayya ta duba yiwuwar biyan diyya ga wadanda wannan lamarin ya shafa.

Da yake jawabi a yayin ziyarar ministan Manajan daraktan kamfanin rarraba wutar ta nan jahar Kano KEDCO Abubakar Yusuf, ya tabbatarwa da al’ummar Kano cewa kamfanin KEDCO ya shirya tsaf dan ganin an Samu wuta wadacciya a fadin jahohin Kano da Katsina da Jigawa.

Ministan ya ziyarci gidan rarraba wuta na Kumbotso da tashar wuta mai amfani da hasken rana ta zawaciki wato Bagaja Renewable Energy Company.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp