Home General Tinubu zai yi hadin Gwiwa da Abba Gida Gida don samar da...

Tinubu zai yi hadin Gwiwa da Abba Gida Gida don samar da wutar Lantarki

Gwamnatin tarayya Nijeriya na shirin yin hadin gwiwa da Gwamnatin Kano, don samar da tashar wutar lantarki mai zaman kanta a jihar dake arewacin kasar.

Ministan makamashi na kasa Chief Adebayo Adelabu ne ya bayyana hakan a yayin wata ziyara da ya kai jihar a yammacin ranar Alhamis, inda yace wannan kudiri zai taimaka matuka wajen kaucewa matsalolin wutar lantarki a jihar dake matsayin cibiyar kasuwanci a yankin da kuma kaucewa sake lalacewar wutar da ya jefa da dama cikin halin kakanakayi.

Wannan na zuwa ne bayan da aka kwashe tsahon kwanaki a yankin babu wutar ta lantarki, lamarin da ya shafi jihohi 17, abin da ya jefa al’ummar cikin duhu da asara mai yawa a fannin kasuwancin.

Hukumomi sun yi zargin cewa ‘yanbindiga ne suka tunkuɗe layin wutar da ke kai wa arewa maso yamma, da arewa maso gabas, da wani ɓangare na arewa ta tsakiya wutar.

Da yake jawabi a lokacin da ya tarbi ministan Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir yusuf wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan fadar Gwamantin Kano, Mal. Shehu wada Sagagi, ya nuna damuwar sa matuka kan halin da A’ummar jihar Kano suka shiga bisa daukewar wutar lantakin.

“daukewar wutar lantarkin nan ya saka al’ummar mu cikin mawuyacin hali wanda ya haifar da asarar mai dumbin yawa”

Ya kuma bukaci gwamnatin tarayya ta duba yiwuwar biyan diyya ga wadanda wannan lamarin ya shafa.

Da yake jawabi a yayin ziyarar ministan Manajan daraktan kamfanin rarraba wutar ta nan jahar Kano KEDCO Abubakar Yusuf, ya tabbatarwa da al’ummar Kano cewa kamfanin KEDCO ya shirya tsaf dan ganin an Samu wuta wadacciya a fadin jahohin Kano da Katsina da Jigawa.

Ministan ya ziyarci gidan rarraba wuta na Kumbotso da tashar wuta mai amfani da hasken rana ta zawaciki wato Bagaja Renewable Energy Company.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp