Home General Tinubu zai yi hadin Gwiwa da Abba Gida Gida don samar da...

Tinubu zai yi hadin Gwiwa da Abba Gida Gida don samar da wutar Lantarki

Gwamnatin tarayya Nijeriya na shirin yin hadin gwiwa da Gwamnatin Kano, don samar da tashar wutar lantarki mai zaman kanta a jihar dake arewacin kasar.

Ministan makamashi na kasa Chief Adebayo Adelabu ne ya bayyana hakan a yayin wata ziyara da ya kai jihar a yammacin ranar Alhamis, inda yace wannan kudiri zai taimaka matuka wajen kaucewa matsalolin wutar lantarki a jihar dake matsayin cibiyar kasuwanci a yankin da kuma kaucewa sake lalacewar wutar da ya jefa da dama cikin halin kakanakayi.

Wannan na zuwa ne bayan da aka kwashe tsahon kwanaki a yankin babu wutar ta lantarki, lamarin da ya shafi jihohi 17, abin da ya jefa al’ummar cikin duhu da asara mai yawa a fannin kasuwancin.

Hukumomi sun yi zargin cewa ‘yanbindiga ne suka tunkuɗe layin wutar da ke kai wa arewa maso yamma, da arewa maso gabas, da wani ɓangare na arewa ta tsakiya wutar.

Da yake jawabi a lokacin da ya tarbi ministan Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir yusuf wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan fadar Gwamantin Kano, Mal. Shehu wada Sagagi, ya nuna damuwar sa matuka kan halin da A’ummar jihar Kano suka shiga bisa daukewar wutar lantakin.

“daukewar wutar lantarkin nan ya saka al’ummar mu cikin mawuyacin hali wanda ya haifar da asarar mai dumbin yawa”

Ya kuma bukaci gwamnatin tarayya ta duba yiwuwar biyan diyya ga wadanda wannan lamarin ya shafa.

Da yake jawabi a yayin ziyarar ministan Manajan daraktan kamfanin rarraba wutar ta nan jahar Kano KEDCO Abubakar Yusuf, ya tabbatarwa da al’ummar Kano cewa kamfanin KEDCO ya shirya tsaf dan ganin an Samu wuta wadacciya a fadin jahohin Kano da Katsina da Jigawa.

Ministan ya ziyarci gidan rarraba wuta na Kumbotso da tashar wuta mai amfani da hasken rana ta zawaciki wato Bagaja Renewable Energy Company.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp