Home General Majalisar tattalin arzikin Najeriya ta shawarci Tinubu ya dakatar da ƙudirin harajin...

Majalisar tattalin arzikin Najeriya ta shawarci Tinubu ya dakatar da ƙudirin harajin VAT

Majalisar tattalin arzikin Najeriya NEC ta shawarci shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya janye ƙudurin yi wa harajin VAT garambawul da ya aika majalisar dokokin ƙasa domin a samu isasshen lokacin da za a tattauna tare da fahimtar juna game da abin da ake nufi gyara VAT ɗin.

Tun da farko gwamnonin Arewa da sarakunan yankin sun yi zama na musamman a Kaduna tare da wasu masu ruwa da tsaki a yankin, inda suka yi fatali da ƙudirin na shugaban ƙasa.

Majalisar ta bayyana hakan ne bayan zamanta na 145 a ƙarƙashin mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima a Abuja.

Majalisar ta ɗauki wannan matakin ne bayan shugaban kwamitin shugaban ƙasa na musamman kan tsare-tsare da yi wa haraji garambawul, Mista Taiwo Oyedele ya gabatar da jawabi game da tsare-tsaren da suke yi, inda majalisar ta ce akwai buƙatar a samu ƙarin lokaci domin tattaunawa tare da fahimtar juna.

Haka kuma Kashim Shettima ya ce za su ɗauki matakai da suka dace domin tabbatar da ba a sake samun irin katsewar lantarkin da aka fuskanta ba a kwanankin baya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp