Home General Majalisar tattalin arzikin Najeriya ta shawarci Tinubu ya dakatar da ƙudirin harajin...

Majalisar tattalin arzikin Najeriya ta shawarci Tinubu ya dakatar da ƙudirin harajin VAT

Majalisar tattalin arzikin Najeriya NEC ta shawarci shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya janye ƙudurin yi wa harajin VAT garambawul da ya aika majalisar dokokin ƙasa domin a samu isasshen lokacin da za a tattauna tare da fahimtar juna game da abin da ake nufi gyara VAT ɗin.

Tun da farko gwamnonin Arewa da sarakunan yankin sun yi zama na musamman a Kaduna tare da wasu masu ruwa da tsaki a yankin, inda suka yi fatali da ƙudirin na shugaban ƙasa.

Majalisar ta bayyana hakan ne bayan zamanta na 145 a ƙarƙashin mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima a Abuja.

Majalisar ta ɗauki wannan matakin ne bayan shugaban kwamitin shugaban ƙasa na musamman kan tsare-tsare da yi wa haraji garambawul, Mista Taiwo Oyedele ya gabatar da jawabi game da tsare-tsaren da suke yi, inda majalisar ta ce akwai buƙatar a samu ƙarin lokaci domin tattaunawa tare da fahimtar juna.

Haka kuma Kashim Shettima ya ce za su ɗauki matakai da suka dace domin tabbatar da ba a sake samun irin katsewar lantarkin da aka fuskanta ba a kwanankin baya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp