Home General Majalisar tattalin arzikin Najeriya ta shawarci Tinubu ya dakatar da ƙudirin harajin...

Majalisar tattalin arzikin Najeriya ta shawarci Tinubu ya dakatar da ƙudirin harajin VAT

Majalisar tattalin arzikin Najeriya NEC ta shawarci shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya janye ƙudurin yi wa harajin VAT garambawul da ya aika majalisar dokokin ƙasa domin a samu isasshen lokacin da za a tattauna tare da fahimtar juna game da abin da ake nufi gyara VAT ɗin.

Tun da farko gwamnonin Arewa da sarakunan yankin sun yi zama na musamman a Kaduna tare da wasu masu ruwa da tsaki a yankin, inda suka yi fatali da ƙudirin na shugaban ƙasa.

Majalisar ta bayyana hakan ne bayan zamanta na 145 a ƙarƙashin mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima a Abuja.

Majalisar ta ɗauki wannan matakin ne bayan shugaban kwamitin shugaban ƙasa na musamman kan tsare-tsare da yi wa haraji garambawul, Mista Taiwo Oyedele ya gabatar da jawabi game da tsare-tsaren da suke yi, inda majalisar ta ce akwai buƙatar a samu ƙarin lokaci domin tattaunawa tare da fahimtar juna.

Haka kuma Kashim Shettima ya ce za su ɗauki matakai da suka dace domin tabbatar da ba a sake samun irin katsewar lantarkin da aka fuskanta ba a kwanankin baya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp