Home General Gwamnatin Tarayya Ta Raba Kuɗin Tallafi ₦25,000 Ga Ƴan Najeriya Miliyan 25

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Kuɗin Tallafi ₦25,000 Ga Ƴan Najeriya Miliyan 25

Gwamnatin Tarayya ta sanar da cewa sama da ƴan Najeriya miliyan 25 ne suka ci gajiyar shirin raba kuɗin tallafi na ₦25,000 zuwa yanzu, abin da ke temakawa matuƙa yayin da ake aiwatar da sauye-sauyen tattalin arziki.

Ministan Kuɗi, Mista Wale Edun ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da aka yi a Fadar Shugaban Ƙasa a ranar Alhamis.

Bayanin ya biyo bayan taron Majalisar Tattalin Arziƙi ta Ƙasa (NEC), wanda Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya jagoranta a Fadar Shugaban Ƙasa dake Abuja.

Da yake bayyana matakan da gwamnatin ke ɗauka domin rage wa ƴan Najeriya nauyin tattalin arziƙi a sakamakon cire tallafin man fetur da sauran tsare-tsaren sauye-sauyen kuɗaɗe, Mista Edun ya yi nuni da ƙoƙarin rage wa mutane ƙunci da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ke yi.

“Ana hasashen cewa gidaje miliyan biyar ne suka ci gajiyar shirin raba kuɗi kai-tsaye,” in ji shi, yana mai jaddada yawan waɗanda suka amfana da shirin.

Bugu da ƙari, Mista Edun ya bayyana cewa kimanin mutane 11,000 ne suka karɓi naira biliyan 3.5 a ƙarƙashin tsarin ba da rance na kayan amfani a cikin kwanaki biyar da suka gabata.

Haka kuma, ya sanar da cewa fiye da naira biliyan 90 sun samu shiga cikin shirin ba da rancen ɗalibai, wanda ke taimaka wa ɗalibai kusan rabin miliyan na Najeriya wajen cimma burin iliminsu.

Taron NEC ɗin ya kuma tattauna batun matsalar ambaliyar ruwa da ta addabi al’umma a faɗin Najeriya.

Mataimakin Shugaban Ƙasa Shettima, tare da Majalisar, sun bayyana damuwa matuƙa kan asarar rayuka da kuma asarar dukiyoyi da aka samu.

Ambaliyar ruwan ta yi sanadiyyar mutuwar aƙalla ƴan Najeriya 321 a faɗin jihohi 34, inda fiye da mutane miliyan 1.2 suka rasa muhallansu kuma fiye da gidaje miliyan ɗaya suka lalace.

Bayan taron, Gwamnan Jihar Anambra, Farfesa Charles Soludo, ya yi jawabi ga manema labarai, inda ya bayyana yadda ambaliyar ta shafi rayuwar jama’a da kuma harkar noma.

“Ana samun asara sosai a gonaki, inda ambaliyar ta wanke gonaki, ta bar dubban ƴan Najeriya ba tare da gidaje ko hanyoyin samun abinci ba,” in ji shi.

Majalisar Tattalin Arziƙi ta Ƙasa ta bukaci ɗaukar matakin gaggawa don rage wahalhalun da waɗanda ambaliyar ta shafa ke fuskanta, sannan ta roƙi hukumomin gwamnati su ƙara ƙoƙari wajen samar da tallafi ga waɗanda abin ya shafa.

Waɗannan matakan na nuna sadaukarwar gwamnati wajen tallafa wa ƴan Najeriya a lokacin wahala, ko ta hanyar ba da tallafin kuɗi ko kuma ɗaukar matakin gaggawa domin tallafa wa waɗanda lamarin ya shafa, duba da irin ƙalubalen tattalin arziki da na muhalli da ake fuskanta a wannan lokaci.

To sai dai kuma, abin tambayar shine, ko tsare-tsaren na tasiri? Abin da za a jira a gani kenan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp