Home General Kuyi Hattara Da IMF – Sakon Farfesa Jega Ga Najeriya

Kuyi Hattara Da IMF – Sakon Farfesa Jega Ga Najeriya

Tsohon shugaban hukumar zaɓe ta Najeriya, Farfesa Attahiru Jega ya yi kira ga gwamnatin Najeriya da ta yi hattara da rungumar dukkan shawarwarin da Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ke bayarwa.

Farfesa Jega ya bayyana hakan ne a yayin zantawar sa da BBC Hausa, inda ya ce shawarwarin suna ƙunshe da wasu abubuwa da za su iya jefa ƙasashe masu tasowa cikin yanayi mara kyau.

Ya kuma kara da cewa lallai akwai alfanun da ke tattare da hulɗa da irin waɗannan cibiyoyin, sai dai kuma ƙasashen da suke karɓar shawarwarin, Najeriya akwai buƙatar su yi hattara, ka da hulɗar ta jefa ƙasar cikin matsin rayuwar da za’a daɗe ba’a fita ba.

“Tun a 1992 lokacin da nake jagorantar ƙungiyar ASUU asusun lamunin na duniya ya tattara ministoci na ilimi suka yi taro a Kenya, suka ce ai Najeriya ba ta buƙatar jami’o’i, suka ce karatun da ya kamata a yi shi ne abin da suke kira “technical education” wato ilimi na fasaha da ƙere-ƙere, ba wai ilimi mai zurfi irin na jami’a ba. Irin wannan shawara da gwamnatin can baya ta yi na cikin abubuwan da suka janyo mana taɓarɓarewar ilimi a halin yanzu,” in ji shi.

Jega ya ce akwai buƙatar a yi la’akari da cewa suna bayar da shawarwari ne game da abubuwan da suke ganin za su fi amfani a gare su ba wai ga ƙasashen masu tasowa ba.

Tsohon malamin jami’ar ya ƙara da cewa daga cikin ƙalubalen da Najeriya ke fuskanta akwai rashin shugabanci nagari, inda ya ce tun da aka dawo tsarin Demokraɗiyya, Jam’iyyu ba su cika tsayar da ƴan takara da suka cancanta ba domin fuskantar ƙalubale.

“Mun san lokacin da aka yi wasu tsare-tsare na tsuke bakin aljihu da ake kira “Structural Adjustement Program”, waɗanda bankunan suka kawo mana tun wurin 1992, irin tsare-tsaren da suke kawowa, su ce gwamnati ta fitar da hannunta wurin inganta rayuwar jama’a ko ba su tallafi, sai dai komai a bar shi a kasuwa, kuma yadda kasuwa ta yi haka za a yi”.

“Tun lokacin ne suke bayar da irin waɗannan shawarwari, adan haka muna kyautata zaton a Najeriya ma irin abun da suke faɗa ke nan yanzu.”

Da aka bayyana masa cewa IMF ta zare hannunta daga batun cire tallafin man fetur, Jega ya ce, “To Allahu ne mafi sani, amma dai an riga an san su, kuma an san abun da suka yi a baya kuma dabarun suna da yawa.

A karshe ya ce wani lokacin ƙeƙe da ƙeƙe za’a yi, wani lokacin cikin hikima za su gabatar da abubuwa a zo a ɗauka, daga baya su ce a’a ai ba haka ba, amma dai ayi hattara, inji Farfesa Jega.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp