Home General Peter Obi ya bukaci yin bincike kan tauye hakkin kananan yara a...

Peter Obi ya bukaci yin bincike kan tauye hakkin kananan yara a Nijeriya

Jagoran jam’iyyar adawa ta LP a Najeriya, Peter Obi ya yi kira ga mahukuntar ƙasar, musamman ministan shari’a da rundunar ‘yansanda da DSS da kuma hukumar kare haƙƙin bil-adama su gudanar da cikakken bincike kan ”azabtarwar da aka yi wa ƙananan yaran da aka gurfanar a gaban kotu bisa zargin cin amanar ƙasa.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Mista Obi ya ce bidiyon yaran da aka yaɗa a gaban kotu abin tayar da hankali ne.

”Halin da yaran ke ciki na yunwa da galabaita abin tayar da hankali ne ga duk wani mai hankali a ƙasar nan”, in ji shi.

A yau ne dai ‘yansandan Najeriya suka gabatar da wasu mutane ciki har da ƙananan yara a gaban kotu bisa zargin laifuka masu yawa ciki har da cin amanar ƙasa, kimanin wata uku bayan kamasu.

Yadda aka gabatar da yaran ya janyo ka-ce-na-ce a faɗin ƙasar, musamman yadda aka ga wasu daga cikin ƙananna yaran cikin mawuyacin hali.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp