Home General Peter Obi ya bukaci yin bincike kan tauye hakkin kananan yara a...

Peter Obi ya bukaci yin bincike kan tauye hakkin kananan yara a Nijeriya

Jagoran jam’iyyar adawa ta LP a Najeriya, Peter Obi ya yi kira ga mahukuntar ƙasar, musamman ministan shari’a da rundunar ‘yansanda da DSS da kuma hukumar kare haƙƙin bil-adama su gudanar da cikakken bincike kan ”azabtarwar da aka yi wa ƙananan yaran da aka gurfanar a gaban kotu bisa zargin cin amanar ƙasa.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Mista Obi ya ce bidiyon yaran da aka yaɗa a gaban kotu abin tayar da hankali ne.

”Halin da yaran ke ciki na yunwa da galabaita abin tayar da hankali ne ga duk wani mai hankali a ƙasar nan”, in ji shi.

A yau ne dai ‘yansandan Najeriya suka gabatar da wasu mutane ciki har da ƙananan yara a gaban kotu bisa zargin laifuka masu yawa ciki har da cin amanar ƙasa, kimanin wata uku bayan kamasu.

Yadda aka gabatar da yaran ya janyo ka-ce-na-ce a faɗin ƙasar, musamman yadda aka ga wasu daga cikin ƙananna yaran cikin mawuyacin hali.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp