Home General Kotu ta bayar da umarnin ƙwace dala miliyan biyu da wasu kadarori...

Kotu ta bayar da umarnin ƙwace dala miliyan biyu da wasu kadarori masu alaƙa da Emefiele

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Legas ta bayar da umarnin kammala ƙwace wasu kuɗi kimamin dala miliyan biyu daga wajen tsohon gwamnan babban bankin ƙasar Godwin Emefiele.

Yayin da yake yanke hukuncin, alƙalin kotun mai shari’a, Dehinde Dipeolu ya kuma bayar da umarnin ƙwace wasu kadarori bakwai masu alaƙa da tsohon gwamnan na CBN, da kuwa wasu takardu mallakar hannayen jari.

Mai shari’a Dipeolu ya ba da umarnin ne bayan buƙatar hakan daga lauyoyin hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC.

Kotun ta ƙwace kadarorin ne bayan da ta ce tsohon gwamnan na CBN ya kasa alaƙanta abin da ta kira ‘halastaccen samunsa’ a lokacin da yake aiki da bankin Zenith da kuma CBN da kuma mallakar kadarorin.

Haka kuma kotun ta ce mista Emefiele ya kasa gabatar da takardun da ke nuna cewa kadarorin mallakarsa ne.

A ranar 15 ga watan Agustan da ya gabata ne kotun ta bayar da umarnin wucin gadi ga EFCC na ƙwace kuɗin da suka kai dala miliyan 2.045 da kadarorin bakwai da takardun mallakar hannayen jarin bayan sauraron ƙarafin da lauyoyin hukumar suka gabatar mata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp