Home General Kotu ta bayar da umarnin ƙwace dala miliyan biyu da wasu kadarori...

Kotu ta bayar da umarnin ƙwace dala miliyan biyu da wasu kadarori masu alaƙa da Emefiele

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Legas ta bayar da umarnin kammala ƙwace wasu kuɗi kimamin dala miliyan biyu daga wajen tsohon gwamnan babban bankin ƙasar Godwin Emefiele.

Yayin da yake yanke hukuncin, alƙalin kotun mai shari’a, Dehinde Dipeolu ya kuma bayar da umarnin ƙwace wasu kadarori bakwai masu alaƙa da tsohon gwamnan na CBN, da kuwa wasu takardu mallakar hannayen jari.

Mai shari’a Dipeolu ya ba da umarnin ne bayan buƙatar hakan daga lauyoyin hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC.

Kotun ta ƙwace kadarorin ne bayan da ta ce tsohon gwamnan na CBN ya kasa alaƙanta abin da ta kira ‘halastaccen samunsa’ a lokacin da yake aiki da bankin Zenith da kuma CBN da kuma mallakar kadarorin.

Haka kuma kotun ta ce mista Emefiele ya kasa gabatar da takardun da ke nuna cewa kadarorin mallakarsa ne.

A ranar 15 ga watan Agustan da ya gabata ne kotun ta bayar da umarnin wucin gadi ga EFCC na ƙwace kuɗin da suka kai dala miliyan 2.045 da kadarorin bakwai da takardun mallakar hannayen jarin bayan sauraron ƙarafin da lauyoyin hukumar suka gabatar mata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp