Home DUNIYA Majalisar Dokokin Kano ta Dakatar da Ciyaman din Rano

Majalisar Dokokin Kano ta Dakatar da Ciyaman din Rano

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Majalisar dokokin jihar Kano ta dakatar da shugaban karamar hukumar Rano Alhaji Naziru Ya’u na tsawon watanni uku sakamakon rashin Iya tafiyar da mulki da karya dokokin aiki tare da umartar sa ya mika aiki ga mataimakin sa.

Majalisar ta dauki wannan matakin ne yayin zaman da ta gudanar a Wannan Rana ta Laraba.

Rahotanni dai sun nuna cewa ana zargin Shugaban karamar hukumar da aka dakatar da sayar da takin zamani ko karkatar da shi wanda gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya rabawa kananan hukumomin kano a watan Yulin da ya gabata.

Ko wacce karamar hukuma ta samu tirela uku na takin zamanin mai dauke da buhu 600 ko wacce mota

Haka kuma Majalisar ta yi karatu na daya akan kudirin dokar kwarya kwaryar kasafin kudi na wannan shekarar da gwamna Abba Kabir Yusuf ya aike mata wanda yakai fiye da naira biliyan dari da sittin da tara.

Akawun majalisar Alhaji Bashir Idris Diso shine yayi karatun a yayin zaman majalissar na yau laraba.

Zaman majalissar Wanda shugaban ta Alhaji Jibril Isma’il Falgore ya jagoranta ya amince Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nada Alhaji Sa’id Yahaya a matsayin shugaban hukumar karbar korafi da hana cin hanci da rashawa ta jihar Kano.

Hakan ya biyo bayan rahoton da shugaban kwamitin karbar kirafi na majalissar kuma dan Majalissa mai wakiltar karamar hukumar Dala Alhaji Lawan Hussaini Chediyar Yan Gurasa ya gabatar.

Ya ce Alhaji Sa’id Yahaya ya cika dukkanin Ka’idojin da doka ta tanadar kafin nada mutum a matsayin shugaban hukumar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp