Home Labarai Ƙananan dillalan mai sun zargi shugabanninsu da yiwa Matatar Dangote zagon ƙasa

Ƙananan dillalan mai sun zargi shugabanninsu da yiwa Matatar Dangote zagon ƙasa

Matatar Dangote

Ƙananan dillalan man fetur a Najeriya sun zargi shugabannin su da neman yiwa Matatar Dangote zagon ƙasa a yunƙurin ta na jigila da kuma rarraba tataccen mai zuwa sassan ƙasar.

Daya daga cikin ƙananan dillalan Alhaji Ladan Abdullahi Garkuwa ya ce matakin na Dangote zai bai wa masu ƙaramin ƙarfi irin su damar dawo da karsashin su na dillancin man, la’akari da cewar tsadar man ya sa basa iya sayensa kamar yadda suke yi a baya.

Garkuwa ya ce da yana da gidajen mai guda biyar yanzu haka, amma tsadarsa ya sa ba ya iya sayen mota guda da zai sayar.

Dillalin ya ce yanzu da wannan sabon tsari na Dangote wanda zai dinga kai musu man kai tsaye zuwa gidajen man su, inda har sai sun sayar su biya shi, matakin zai ba shi damar karbar man a gidajen man sa guda biyar domin ci gaba da kasuwancinsa.

Dan kasuwan ya ce wannan mataki zai ba shi damar ɗaukar ƙarin ma’aikata waɗanda su ma za su amfana da tsarin, wadda za ta taimaka wajen sauƙaƙa wahalar man.garkuwa ya ce abin takaici ne yadda manyan dilallan man ke adawa da shirin Dangoten, wanda suke kallonsa a matsayin babbar barazana ga harkokin su, musamman  ganin yadda suka mamaye harkar man suke kuma cin karen su babu babbaka.

Tuni matatar Dangote ta karɓi wasu daga cikin motocin da ta sayo daga ƙasar China da za su yi aikin jigilar man zuwa sassan Najeriya, a yunƙurin sauƙaƙawa jama’ar ƙasar samun tacaccen man da suke sarrafawa.

A baya, manyan dillalan man a Najeriya, sun gabatar da ƙorafin adawa da shirin Dangote na sayo motocin da za su dinga safarar man, inda suka zarge shi da yunƙurin mamaye kasuwar.

Wanan bai sanya Dangoten ƙasa a gwuiwa ba, wajen ci gaba da sayo motocin waɗanda tuni suka isa Najeriya domin fara aiki.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp