Home DUNIYA Ƴan bindiga sun kashe mutum biyar a jihar Filato

Ƴan bindiga sun kashe mutum biyar a jihar Filato

'Yan Ta'adda

Rahotanni daga jihar Filato na bayyana cewa wasu da ake zargin ƴan bindiga ne sun hallaka mutum biyar a karamar hukumar Bokkos na jihar.

Lamarin wanda ya faru a ranar Lahadi da daddare na zuwa ne kwanaki 11 bayan kai hari makamancinsa a karamar hukumar tare da kashe mutum bakwai.

an ruwaito cewa shugaban ƙungiyar ci gaban al’ummar Bokkos, Farmasum Fuddang, ya tabbatar da faruwar lamarin da kuma yin Alla-wadai da shi.

Ya ce an yi mutanen da aka kashen kwantan ɓauna lokacin da suke balaguro daga garin Mbar zuwa kauyen Koh na jihar.

Ƴan bindigar sun je ne a kan babura inda suka yi wa garin dirar mikiya da misalin karfe 7 na yammaci.

Fuddang ya soki jami’an tsaro saboda rashin mayar da martani a kan lokaci, inda ya ce kafin zuwarsu maharan sun riga da sun tsere.

Ya kuma nuna damuwar cewa irin waɗannan hare-hare da ake kai wa za su iya ɗaiɗaita al’ummomin yankin gabaki ɗaya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp