Home DUNIYA Ƴan bindiga sun kashe mutum biyar a jihar Filato

Ƴan bindiga sun kashe mutum biyar a jihar Filato

'Yan Ta'adda

Rahotanni daga jihar Filato na bayyana cewa wasu da ake zargin ƴan bindiga ne sun hallaka mutum biyar a karamar hukumar Bokkos na jihar.

Lamarin wanda ya faru a ranar Lahadi da daddare na zuwa ne kwanaki 11 bayan kai hari makamancinsa a karamar hukumar tare da kashe mutum bakwai.

an ruwaito cewa shugaban ƙungiyar ci gaban al’ummar Bokkos, Farmasum Fuddang, ya tabbatar da faruwar lamarin da kuma yin Alla-wadai da shi.

Ya ce an yi mutanen da aka kashen kwantan ɓauna lokacin da suke balaguro daga garin Mbar zuwa kauyen Koh na jihar.

Ƴan bindigar sun je ne a kan babura inda suka yi wa garin dirar mikiya da misalin karfe 7 na yammaci.

Fuddang ya soki jami’an tsaro saboda rashin mayar da martani a kan lokaci, inda ya ce kafin zuwarsu maharan sun riga da sun tsere.

Ya kuma nuna damuwar cewa irin waɗannan hare-hare da ake kai wa za su iya ɗaiɗaita al’ummomin yankin gabaki ɗaya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp