Home DUNIYA Ƴan bindiga sun kashe mutum biyar a jihar Filato

Ƴan bindiga sun kashe mutum biyar a jihar Filato

'Yan Ta'adda

Rahotanni daga jihar Filato na bayyana cewa wasu da ake zargin ƴan bindiga ne sun hallaka mutum biyar a karamar hukumar Bokkos na jihar.

Lamarin wanda ya faru a ranar Lahadi da daddare na zuwa ne kwanaki 11 bayan kai hari makamancinsa a karamar hukumar tare da kashe mutum bakwai.

an ruwaito cewa shugaban ƙungiyar ci gaban al’ummar Bokkos, Farmasum Fuddang, ya tabbatar da faruwar lamarin da kuma yin Alla-wadai da shi.

Ya ce an yi mutanen da aka kashen kwantan ɓauna lokacin da suke balaguro daga garin Mbar zuwa kauyen Koh na jihar.

Ƴan bindigar sun je ne a kan babura inda suka yi wa garin dirar mikiya da misalin karfe 7 na yammaci.

Fuddang ya soki jami’an tsaro saboda rashin mayar da martani a kan lokaci, inda ya ce kafin zuwarsu maharan sun riga da sun tsere.

Ya kuma nuna damuwar cewa irin waɗannan hare-hare da ake kai wa za su iya ɗaiɗaita al’ummomin yankin gabaki ɗaya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp