Home General An samu raguwar hauhawar farashi a watan Agusta – NBS

An samu raguwar hauhawar farashi a watan Agusta – NBS

Hukumar kididdiga ta Najeriya (NBS) ta ce an samu raguwar hauhawar farashi a ƙasar daga kashi 33.40 a watan Yuni zuwa kashi 32.15 a watan Agusta.

A cewar wani rahoto da NBS ɗin ta fitar ranar Litinin, ta ce an samu raguwar ta kashi 32.15 ne a watan Agustan 2024, yayin da farashin abinci kuma ya kasance a kashi 37.52 a watan na Agusta.

“Alkaluman da muka tattara sun nuna cewa an samu raguwar kashi 1.25 idan aka kwatanta da n watan Yulin 2024,” in ji rahoton.

NBS ta ce farashin kayan abinci a watan Agustan 2024 ya kai kashi 37.52, idan aka kwatanta da adadin da aka samu a watan Agustan 2023 na kashi 29.34.

Ta ce an samu hauhawar farashin kayan abincin ne sakamakon tashin farashin kayayyaki kamar burodi da masara da hatsi da dawa da dankalin turawa da rogo da dabino da sauransu.

Hukumar ta ce farashin abinci a watan Agustan 2024 ya kasance a kashi 2.37 wanda ya nuna raguwa da kashi 0.10 idan aka kwatanta da adadin da aka samu a watan Yulin 2024 na kashi 2.47.

Ta ce za a iya danganta raguwar da faɗuwar farashin kayayyaki kamar sikari da ganyen shayi da man gyaɗa da madara da dawa ganyayyaki da sauransu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp