Home General An samu raguwar hauhawar farashi a watan Agusta – NBS

An samu raguwar hauhawar farashi a watan Agusta – NBS

Hukumar kididdiga ta Najeriya (NBS) ta ce an samu raguwar hauhawar farashi a ƙasar daga kashi 33.40 a watan Yuni zuwa kashi 32.15 a watan Agusta.

A cewar wani rahoto da NBS ɗin ta fitar ranar Litinin, ta ce an samu raguwar ta kashi 32.15 ne a watan Agustan 2024, yayin da farashin abinci kuma ya kasance a kashi 37.52 a watan na Agusta.

“Alkaluman da muka tattara sun nuna cewa an samu raguwar kashi 1.25 idan aka kwatanta da n watan Yulin 2024,” in ji rahoton.

NBS ta ce farashin kayan abinci a watan Agustan 2024 ya kai kashi 37.52, idan aka kwatanta da adadin da aka samu a watan Agustan 2023 na kashi 29.34.

Ta ce an samu hauhawar farashin kayan abincin ne sakamakon tashin farashin kayayyaki kamar burodi da masara da hatsi da dawa da dankalin turawa da rogo da dabino da sauransu.

Hukumar ta ce farashin abinci a watan Agustan 2024 ya kasance a kashi 2.37 wanda ya nuna raguwa da kashi 0.10 idan aka kwatanta da adadin da aka samu a watan Yulin 2024 na kashi 2.47.

Ta ce za a iya danganta raguwar da faɗuwar farashin kayayyaki kamar sikari da ganyen shayi da man gyaɗa da madara da dawa ganyayyaki da sauransu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp