Home General Tinubu ya kai ziyara Maiduguri don jajantawa al’umma iftila’in ambaliya

Tinubu ya kai ziyara Maiduguri don jajantawa al’umma iftila’in ambaliya

Shugaba Bola Tinubu ya kai ziyara birnin Maiduguri domin jajantawa al’ummar jihar Borno iftila’in ambaliyar da ya afka musu.

Ziyarar tasa na zuwa ne kwanaki shida bayan mummunar ambaliyar da birnin ya fuskanta wanda rabon a ga haka tun bayan shekara 30 da suka wuce.

Bayan isarsa birnin, kai-tsaye ya garzaya ɗaya daga cikin sansanonin da aka tsugunar da waɗanda lamarin ya ɗaiɗaita domin jajanta musu.

Tinubu ya yi alkawarin cewa gwamnatinsa za ta tallafawa mutanen.

“Ina son tabbatar muku da cewa za mu tallafa muku domin rage raɗadin da kuka shiga sakamakon wannan iftila’i,” in ji Tinubu.

Daga bisani, Tinubu ya ziyarci fadar Mai Martaba Shehun Borno, Alh Umar Garbai Ibn El-Kanemi tare da rakiyar gwamna Babagana Zulum domin jajantawa Basaraken kan al’amarin da ya faru.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp