Home General Tinubu ya kai ziyara Maiduguri don jajantawa al’umma iftila’in ambaliya

Tinubu ya kai ziyara Maiduguri don jajantawa al’umma iftila’in ambaliya

Shugaba Bola Tinubu ya kai ziyara birnin Maiduguri domin jajantawa al’ummar jihar Borno iftila’in ambaliyar da ya afka musu.

Ziyarar tasa na zuwa ne kwanaki shida bayan mummunar ambaliyar da birnin ya fuskanta wanda rabon a ga haka tun bayan shekara 30 da suka wuce.

Bayan isarsa birnin, kai-tsaye ya garzaya ɗaya daga cikin sansanonin da aka tsugunar da waɗanda lamarin ya ɗaiɗaita domin jajanta musu.

Tinubu ya yi alkawarin cewa gwamnatinsa za ta tallafawa mutanen.

“Ina son tabbatar muku da cewa za mu tallafa muku domin rage raɗadin da kuka shiga sakamakon wannan iftila’i,” in ji Tinubu.

Daga bisani, Tinubu ya ziyarci fadar Mai Martaba Shehun Borno, Alh Umar Garbai Ibn El-Kanemi tare da rakiyar gwamna Babagana Zulum domin jajantawa Basaraken kan al’amarin da ya faru.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp