Home General NAWOJ ta taya Al’ummar Nijeriya Murnan Mauludin Annabi Muhammad S.A.W

NAWOJ ta taya Al’ummar Nijeriya Murnan Mauludin Annabi Muhammad S.A.W

Kungiyar mata ‘yan jaridu reshen Kano NAWOJ ta ta bukaci daukacin al’ummar musulmi Nijeriya da su yi koyi da kyawawan halaye na fiyayyen halitta Annabi Muhammadu (S.A.W).

Wannan dai na cikin wata takardar manema labarai da kungiyar ta fitar, mai dauke da sa hannun sakatariyar kungiyar Maryam Muhammad a wani bangare na bikin murnar zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammadu S.A.W.

Sanarwar ta ambaci shugabar kungiyar Kwamared Bahijja Kabara na kira ga mata ‘yan jaridu da su rubanya kokarinsu ta hanyar bin koyarwar Annabi S A W wajen biyayya ga mazajensu da kuma kyautata alaka da makwabta.

Kwamaret Bahijja ta kuma yi kira ga mata da su koya wa ‘ya’yansu tarihin Annabi Muhammadu ​​tare da yin koyi da halayensa domin kyautata rayuwar al’umma.

Hakazalika Kwamared Bahijja Kabara ya yi kira ga masu hannu da shuni da su taimaka wa marasa galihu kamar yadda aka koya daga koyarwar Annabi Muhd. S.A.W

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp