Home General Mazauna Djibo a Burkina Faso sun buƙaci cikakkiyar kariya daga ƴan ta’adda

Mazauna Djibo a Burkina Faso sun buƙaci cikakkiyar kariya daga ƴan ta’adda

Mazauna garin Djibo na lardin Soum a Burkina Faso sun gudanar da zanga-zanga a ranar Lahadi don neman a inganta musu tsaro biyo bayan mummunan harin ta’adanci da aka kai garin.

Mata, maza da yara ne suka  bazama kan titunan garin  a matsayin martani ga kutsen da ƴan bindiga suka yi a gari  amakon da ya gabata, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane 3, waɗanda ƴan ta’addan suka yi wa yankan rago.

Ɗaya  daga cikin masu zanga-zangar da ya bayyana dalilin fitowar su cikin  fushi ta cikin wani hoton bidiyo, ya ce ƴan ta’addan su na yi musu kutse cikin birnin, inda su ke kashe iyaye, matansu da ƴaƴansu.

Dubban mutane ne suka arce daga wasu sassan birnin da ɗan kayayyakin da za su iya ɗibawa, biyo bayan wa’adin da  wata ƙungiyar ƴan ta’adda ta ɗibar musu.

Hotunan da aka wallafa a shafukan dandalin sada zumunta sun nuna ɗimbim mutane a ruɗe su na barin birnin a ƙasa da jakuna.

Wasu mazauna birnin sun ce ƙungiyar ƴan ta’addan ta bai wa al’ummar  su koma yankuna  na 7,8 da 9 na Djibo. Amma waɗannan yankuna sun kasance a ƙarƙashin ikonsu tsawon shekara guda, amma a maimakon haka sai su ka nufi sansanin soji kai tsaye a cewar majiyoyi da dama.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp