Home Labarai An Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta...

An Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta Kashe

Braimah

An Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta Kashe

 

Rundunar sojin Najeriya ta bayyana cewa an binne ɗaya daga cikin manyan jami’anta Birgediya Janar Omo Braimah da sauran sojojin da mayaƙan Boko Haram suka kashe a wani harin da suka kai kan sansanin soji a jihar Borno.

Braimah, wanda shi ne kwamandan ƙaramar rundunar sojin Najeriya ta 29 Join Task Force Brigade da ke aiki ƙarƙashin rundunar Operation Hadin Kai, ya rasa ransa ne a samamen da mayaƙan na Boko Haram suka kai kan sansaninsu da ke garin Benisheikh na yankin ƙaramar hukumar Kaga.

A wani saƙo da ta wallafa a shafinta na facebook, rundunar sojin Najeriya ta ce a yau Laraba 15 ga watan Afrilu ne aka binne Braimah, da kyaftin Ismail da kuma sauran sojojin da suka sadaukar da rayuwarsu a bakin aiki.

An gudanar da jana’zar ne a barikin Maimalari da ke jihar Borno, gaban iyalai da ƴan’uwan mamatan.

Cikin waɗanda suka halarci binne mamatan akwai gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum, da ministan tsaro na Najeriya Christopher Musa da babban hafsan sojin ƙasa na Najeriya da kuma mutane da dama.

Najeriya na ci gaba da fuskantar ƙalubalai daga ƙungiyar Boko Haram wadda a baya-bayan nan ta ƙara ƙaimi wajen kai hare-hare kan cibiyoyin soji da kuma fararen hula a arewa maso gabashin ƙasar.

Ko a ranar Litinin ɗin wannan mako rundunar sojin ta sanar da mutuwar ɗaya daga cikin kwamandojinta yayin wani hari da mayaƙan Boko Haram suka kai kan dakarunta a ƙaramar hukumar Monguno da ke jihar ta Borno.

Boko Haram ta shafe sama da shekara 15 tana ƙaddamar da hare-hare a Najeriya, lamarin da ya yi sanadiyyar rayukan dubban mutane da raba miliyoyi da muhallansu.

Hukumomi a Najeriya na ci gaba da iƙirarin samun nasara kan ƙungiyar, sai dai har yanzu matsalar na ci gaba da haifar da asarar rayuka da dukiya.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp