Home Labarai An Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta...

An Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta Kashe

Braimah

An Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta Kashe

 

Rundunar sojin Najeriya ta bayyana cewa an binne ɗaya daga cikin manyan jami’anta Birgediya Janar Omo Braimah da sauran sojojin da mayaƙan Boko Haram suka kashe a wani harin da suka kai kan sansanin soji a jihar Borno.

Braimah, wanda shi ne kwamandan ƙaramar rundunar sojin Najeriya ta 29 Join Task Force Brigade da ke aiki ƙarƙashin rundunar Operation Hadin Kai, ya rasa ransa ne a samamen da mayaƙan na Boko Haram suka kai kan sansaninsu da ke garin Benisheikh na yankin ƙaramar hukumar Kaga.

A wani saƙo da ta wallafa a shafinta na facebook, rundunar sojin Najeriya ta ce a yau Laraba 15 ga watan Afrilu ne aka binne Braimah, da kyaftin Ismail da kuma sauran sojojin da suka sadaukar da rayuwarsu a bakin aiki.

An gudanar da jana’zar ne a barikin Maimalari da ke jihar Borno, gaban iyalai da ƴan’uwan mamatan.

Cikin waɗanda suka halarci binne mamatan akwai gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum, da ministan tsaro na Najeriya Christopher Musa da babban hafsan sojin ƙasa na Najeriya da kuma mutane da dama.

Najeriya na ci gaba da fuskantar ƙalubalai daga ƙungiyar Boko Haram wadda a baya-bayan nan ta ƙara ƙaimi wajen kai hare-hare kan cibiyoyin soji da kuma fararen hula a arewa maso gabashin ƙasar.

Ko a ranar Litinin ɗin wannan mako rundunar sojin ta sanar da mutuwar ɗaya daga cikin kwamandojinta yayin wani hari da mayaƙan Boko Haram suka kai kan dakarunta a ƙaramar hukumar Monguno da ke jihar ta Borno.

Boko Haram ta shafe sama da shekara 15 tana ƙaddamar da hare-hare a Najeriya, lamarin da ya yi sanadiyyar rayukan dubban mutane da raba miliyoyi da muhallansu.

Hukumomi a Najeriya na ci gaba da iƙirarin samun nasara kan ƙungiyar, sai dai har yanzu matsalar na ci gaba da haifar da asarar rayuka da dukiya.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp