Home Labarai Gwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa Malami

Gwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa Malami

Malami

Gwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa Malami

 

Gwamnatin Tarayya ta sauya zarge-zargen da ta ke yi wa tsohon Ministan Shari’ar ƙasar Abubakar Malami, tare da ɗansa Abdul’aziz inda aka cire zargin ɗaukar nauyin ta’addanci ciki.

A zaman kotun da aka yi a ranar Laraba, Akinlolu Kahinde wakilin hukumar farin kaya ta Naeriya DSS ne ya sanar da kotu kan sauya zargin da ake yi wa Malamin, kuma ya sa aka maye zargin da wani.

Cikin sauyin da aka samu har da cire zargin mallakar makamai.

Shu’aibu Aruwa, mai kare Malami, ya tabbatar da wanda yake karewa ya amince da cire tuhumar tare da sauya ta da wasu wanda aka karanto.

Dama tun lokacin da aka karanta masa tuhumar a baya, ya musanta zargin.

Yanzu an sake ɗage zaman kotun zuwa ranar 26 ga watan Mayu da kuma 15 ga watan Yuni domin ci gaba da saurare.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp