Home Labarai Gwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa Malami

Gwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa Malami

Malami

Gwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa Malami

 

Gwamnatin Tarayya ta sauya zarge-zargen da ta ke yi wa tsohon Ministan Shari’ar ƙasar Abubakar Malami, tare da ɗansa Abdul’aziz inda aka cire zargin ɗaukar nauyin ta’addanci ciki.

A zaman kotun da aka yi a ranar Laraba, Akinlolu Kahinde wakilin hukumar farin kaya ta Naeriya DSS ne ya sanar da kotu kan sauya zargin da ake yi wa Malamin, kuma ya sa aka maye zargin da wani.

Cikin sauyin da aka samu har da cire zargin mallakar makamai.

Shu’aibu Aruwa, mai kare Malami, ya tabbatar da wanda yake karewa ya amince da cire tuhumar tare da sauya ta da wasu wanda aka karanto.

Dama tun lokacin da aka karanta masa tuhumar a baya, ya musanta zargin.

Yanzu an sake ɗage zaman kotun zuwa ranar 26 ga watan Mayu da kuma 15 ga watan Yuni domin ci gaba da saurare.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp