Rundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram Makamai
Rundunar sojin Najeriya ta musanta zargin da ake yi cewa ana bai wa tsofaffin mayaƙan Boko Haram makamai tare da tura su zuwa fagen daga a karkashin shirin gyaran hali.
Read Also:
Mai kula da shirin, Birgediya Janar Yusuf Ali, ya ce zarge-zargen ba gaskiya ba ne, bayan wani bidiyo da aka wallafa a intanet ya nuna wasu tsofaffin mayaƙa, suna fafatawa tare da dakarun soji.
Ya ce mutanen da aka gani a cikin faifan bidiyon ba su da wata alaka da shirin, sannan wurin da aka nuna ba ya ɗaya daga cikin cibiyoyin shirin.
Ƙungiyar Boko Haram dai ta shafe fiye da shekara 10 tana kai hare-hare a yankin arewa maso gabashin Najeriya, inda ta kashe dubban mutane.












