Home General Jam’iyyun siyasa 7 a jihar Bauchi sun sanya hannu a dokar zaman...

Jam’iyyun siyasa 7 a jihar Bauchi sun sanya hannu a dokar zaman lafiya

‘Yan takarar gwamna na jam’iyyun siyasa 7 a jihar Bauchi dake arewa maso gabashin Nijeriya sun sanya hannun a yarjejeniyar zaman lafiya gabanin zaben gwamnoni dake tafe ranar asabar a jihohin kasar.

Taron sanya hannun ya gudana ne a ranar laraba a dakin taro na shalkwatar rundunar ‘yan sanda dake jihar Bauchi.

‘yan takarar da suka sami halartar taron sanya hannun sun hadar da gwamnan jihar dake neman wa’adi na 2 a karkashin inuwar jam’iyyar PDP, sai halliru Dauda Jika, na jam’iyyar NNPP, sai kuma sadique Abubakar na jam’iyyar APC wanda abokin takarar sa Shehu Musa ya wakilce shi a yayin taron.

Sauran sun hadar da ‘yan takarar jam’iyyun LP, YPP, ZLP da kuma PRP, sai dai  a yayin taron ba’a wakilcin jam’iyyun ADC, AC ba.

Haka kuma an hangi wakilcin rundunar sojin Nijeriya, rundunar tsaro ta DSS, jami’an tsaro na Civil Defence, dakarun hukumar hana fasa Kwauri ta Customs, jami’an NDLEA, jami’an dake lura da shige da fice na NIS, da masu lura da ajiya da gyaran hali da tarbiyya.

Kwamishin ‘yan sanda jihar ya karanta sashe na 125 da na 126 na dokar zabe ta 2022 da aka yiwa gyaran fuska matsayin wukar kugun da yayi amfani da ita wajen gargadin ‘yan takarar domin bin doka da Oda a yayin zaben.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp