Home General Jam’iyyun siyasa 7 a jihar Bauchi sun sanya hannu a dokar zaman...

Jam’iyyun siyasa 7 a jihar Bauchi sun sanya hannu a dokar zaman lafiya

‘Yan takarar gwamna na jam’iyyun siyasa 7 a jihar Bauchi dake arewa maso gabashin Nijeriya sun sanya hannun a yarjejeniyar zaman lafiya gabanin zaben gwamnoni dake tafe ranar asabar a jihohin kasar.

Taron sanya hannun ya gudana ne a ranar laraba a dakin taro na shalkwatar rundunar ‘yan sanda dake jihar Bauchi.

‘yan takarar da suka sami halartar taron sanya hannun sun hadar da gwamnan jihar dake neman wa’adi na 2 a karkashin inuwar jam’iyyar PDP, sai halliru Dauda Jika, na jam’iyyar NNPP, sai kuma sadique Abubakar na jam’iyyar APC wanda abokin takarar sa Shehu Musa ya wakilce shi a yayin taron.

Sauran sun hadar da ‘yan takarar jam’iyyun LP, YPP, ZLP da kuma PRP, sai dai  a yayin taron ba’a wakilcin jam’iyyun ADC, AC ba.

Haka kuma an hangi wakilcin rundunar sojin Nijeriya, rundunar tsaro ta DSS, jami’an tsaro na Civil Defence, dakarun hukumar hana fasa Kwauri ta Customs, jami’an NDLEA, jami’an dake lura da shige da fice na NIS, da masu lura da ajiya da gyaran hali da tarbiyya.

Kwamishin ‘yan sanda jihar ya karanta sashe na 125 da na 126 na dokar zabe ta 2022 da aka yiwa gyaran fuska matsayin wukar kugun da yayi amfani da ita wajen gargadin ‘yan takarar domin bin doka da Oda a yayin zaben.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp