Home General Jam’iyyun siyasa 7 a jihar Bauchi sun sanya hannu a dokar zaman...

Jam’iyyun siyasa 7 a jihar Bauchi sun sanya hannu a dokar zaman lafiya

‘Yan takarar gwamna na jam’iyyun siyasa 7 a jihar Bauchi dake arewa maso gabashin Nijeriya sun sanya hannun a yarjejeniyar zaman lafiya gabanin zaben gwamnoni dake tafe ranar asabar a jihohin kasar.

Taron sanya hannun ya gudana ne a ranar laraba a dakin taro na shalkwatar rundunar ‘yan sanda dake jihar Bauchi.

‘yan takarar da suka sami halartar taron sanya hannun sun hadar da gwamnan jihar dake neman wa’adi na 2 a karkashin inuwar jam’iyyar PDP, sai halliru Dauda Jika, na jam’iyyar NNPP, sai kuma sadique Abubakar na jam’iyyar APC wanda abokin takarar sa Shehu Musa ya wakilce shi a yayin taron.

Sauran sun hadar da ‘yan takarar jam’iyyun LP, YPP, ZLP da kuma PRP, sai dai  a yayin taron ba’a wakilcin jam’iyyun ADC, AC ba.

Haka kuma an hangi wakilcin rundunar sojin Nijeriya, rundunar tsaro ta DSS, jami’an tsaro na Civil Defence, dakarun hukumar hana fasa Kwauri ta Customs, jami’an NDLEA, jami’an dake lura da shige da fice na NIS, da masu lura da ajiya da gyaran hali da tarbiyya.

Kwamishin ‘yan sanda jihar ya karanta sashe na 125 da na 126 na dokar zabe ta 2022 da aka yiwa gyaran fuska matsayin wukar kugun da yayi amfani da ita wajen gargadin ‘yan takarar domin bin doka da Oda a yayin zaben.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp