Home DUNIYA UNICEF ta koka da karuwar matan da basa samun wadataccen abinci mai...

UNICEF ta koka da karuwar matan da basa samun wadataccen abinci mai gina jiki

Asusun tallafawa kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya koka da karuwar matan da basa samun wadataccen abinci mai gina ciki musamman masu juna biyu da masu shayarwa.

UNICEF cikin wani rahoto da ya fitar ya ce an samu karuwar matsalar da akalla kashi 25 cikin kasashe 13 galibinsu a Afrika da Asiya, tana mai gargadin cewa idan har ba a dauki matakan magance matsalar ba, ko shakka babu za a samu karuwar haifar jarirai masu ciwon yunwa ko kuma Tamow.

Alkaluman da ke kunshe a rahoton na UNICEF ya nuna cewa adadin mata masu juna biyu da masu shayarwa wadanda basa samun abinci mai gina jiki ya karu daga mutum miliyan 5.5 a shekarar 2020 zuwa miliyan 6 da dubu dari 9 a bana.

Rahoton na UNICEF ya alakanta koma bayan da yadda yakin Rasha a Ukraine ya haddasa yunwa musamman a kasashen da suka dogara da ketare ta fannin abinci.

Rahoton na UNICEF ya ce galibin kasashen da wannan matsala ta fi tsananta na sahun wadanda ko dai su ke fama da rikici ko kuma wadanda ‘yan tawaye ko ‘yan ta’adda ke barazana ga tsaronsu.

Cikin jerin kasashen da rahoton ya bayyana a matsayin kan gaba da ke fama da wannan matsala ta yawaitar matan da basa samun abinci mai gina jiki akwai Afghanistan a kan gaba kana Burkina Faso da Chadi da Habasha sannan Kenya da Mali da Nijar sai Najeriya da Somalia tukuna Sudan da Sudan ta kudu sai kuma Yemen.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp