Home DUNIYA UNICEF ta koka da karuwar matan da basa samun wadataccen abinci mai...

UNICEF ta koka da karuwar matan da basa samun wadataccen abinci mai gina jiki

Asusun tallafawa kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya koka da karuwar matan da basa samun wadataccen abinci mai gina ciki musamman masu juna biyu da masu shayarwa.

UNICEF cikin wani rahoto da ya fitar ya ce an samu karuwar matsalar da akalla kashi 25 cikin kasashe 13 galibinsu a Afrika da Asiya, tana mai gargadin cewa idan har ba a dauki matakan magance matsalar ba, ko shakka babu za a samu karuwar haifar jarirai masu ciwon yunwa ko kuma Tamow.

Alkaluman da ke kunshe a rahoton na UNICEF ya nuna cewa adadin mata masu juna biyu da masu shayarwa wadanda basa samun abinci mai gina jiki ya karu daga mutum miliyan 5.5 a shekarar 2020 zuwa miliyan 6 da dubu dari 9 a bana.

Rahoton na UNICEF ya alakanta koma bayan da yadda yakin Rasha a Ukraine ya haddasa yunwa musamman a kasashen da suka dogara da ketare ta fannin abinci.

Rahoton na UNICEF ya ce galibin kasashen da wannan matsala ta fi tsananta na sahun wadanda ko dai su ke fama da rikici ko kuma wadanda ‘yan tawaye ko ‘yan ta’adda ke barazana ga tsaronsu.

Cikin jerin kasashen da rahoton ya bayyana a matsayin kan gaba da ke fama da wannan matsala ta yawaitar matan da basa samun abinci mai gina jiki akwai Afghanistan a kan gaba kana Burkina Faso da Chadi da Habasha sannan Kenya da Mali da Nijar sai Najeriya da Somalia tukuna Sudan da Sudan ta kudu sai kuma Yemen.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp