Home General Kotu ta bai wa INEC damar sake saita na’urar BVAS bayan karar...

Kotu ta bai wa INEC damar sake saita na’urar BVAS bayan karar PDP da LP

Kotun daukaka kara a Najeriya ta bai wa hukumar INEC izinin sake saita na’urar zabe ta BVAS da aka yi amfani da ita yayin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisu da ya gudana a ranar 25 ga watan da ya gabata.

Yayin zaman kotun na ranar laraba a Abuja fadar gwamnatin Najeriya, zaman da ya gudana karkashin jagorancin alkalai 3 da suka hadar da mai shari’a Joseph Ikyegh da ya karanto hukuncin kotun wanda ya sahalewa INEC saita na’urar ta BVAS gabanin zaben gwamnoni da ‘yan Majalisun jihohi da ke tafe a karshen makon nan.

Kotun ta umarci INEC ta nadi bayanan da ke cikin na’urar ta BVAS tare da adana su a waje mai tsaro baya ga sanya kwafi a rumbunan adana bayananta.

Kafin hukuncin na yau dai, Kotu ta baiwa  dan takarar jam’iyyar adawa ta PDP wato Atiku Abubakar da Peter Obi na jam’iyyar LP damar gudanar da bincike kan na’urar da sauran kayakin zabe masu muhimmanci don samun hujjojin da suke ikirarin an tafka magudi a babban zaben kasar.

‘Yan takarar jam’iyyun adawar da suka zo na biyu da na uku a zaben shugaban kasar na Najeriya wanda Bola Ahmed Tinubu ya yi nasara, sun bukaci isa ga na’urorin zaben ne don tattara hujjoji bayan shigar da karar da ke kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasar.

Sai dai bayan izinin isa ga na’urorin da kotun sauraren karakin zaben Najeriya ta bai wa ‘yan takarar jam’iyyun adawa, INEC ta daukaka kara kan hukuncin bisa kafa hujjoji da illar da hakan zai yi ga zaben Gwamnoni da ke tafe.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp