Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa ya ce kwanakin ɗan bindiga, Bello Turji da sauran manyan ƴanbindiga da suka addabi ƙasar sun kusa ƙarewa a daidai lokacin da sojoji suke cigaba da aiki a jihar Zamfara da sauran jihohin Arewa maso Yamma.
Read Also:
Ya ce kashe Kachalla Halilu Sububu, wanda ƙasurgumin ɗanbindiga ne ya cikin nasarorin da sojojin suke samu.
Janar Christopher ya ƙara da cewa wani aikin soji na musamman mai suna “Fansar Yamma a Arewa maso Yamma,” da za a ƙaddamar ne zai kawo ƙarshen matsalar tsaro a yankin.
Ya ce za a ƙara tura wasu jiragen yaƙi zuwa jihar domin cigaba da aikin sojin, kamar yadda babban hafsan ya bayyana a ziyararsa ga Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal.












