Home General Sojojin Najeriya sun hallaka kwamanda ISWAP “Ibn Kaseer” a Borno

Sojojin Najeriya sun hallaka kwamanda ISWAP “Ibn Kaseer” a Borno

Dakarun sojin Nijeirya karkashin  rundunar Operation hadin kai ta sami nasarar hallaka kwamandan mayakan kungiyar ISWAP, Ibn Kaseer tare da wasu mayakan kungiyar guda uku a wani hari da suka kai dajin Sambisa a safiyar ranar Alhamis.

Zagazola makama ya bayyana cewa wani rahoton sirri ya tabbatar da yadda dakarun sojojin karkashin rundunar sojoji ta 21, sun sami nasarar a yayin wata kora da suka kai a kauyen Kashomeri.

Kwamandan mayakan na ISWAP ta ya addabi al’ummar Geizuwa da Yale ya yi yunkurin samun mafaka a yankin na Kashomeri shi da iyalansa.

Majiyar dai ta tabbatar da cewa bayan bankado maboyar ta sa ne dakarun suka hallaka shi tare da wasu mayakansa guda biyu da aka bayyana a matsayin Bulamadu, sai dai majiyar tace lamarin ya faru ne bayan da mutanen sa suka fita wani aikin taaddanci a yankin Jalumeri.

Haka kuma bayan hallaka kwamandan rundunar ta sami nasarar kubutar da mata hudu da yara kanana, yayin da wasu daga cikin ‘iyalan mayakan na ISWAP suka mika wuya ga dakarun sojojin a Kunduga.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp