Home General NERC ta ci tarar kamfanin AEDC kan tsauwala kuɗin wuta

NERC ta ci tarar kamfanin AEDC kan tsauwala kuɗin wuta

Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Najeriya (NERC) ta ci kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Abuja (AEDC) tarar Naira Biliyan 1.69 bisa laifin tsauwala wa abokan hulɗarsu kuɗin wuta

Gidan talbijin na Channels ya rawaito cewar tarar ta ta’allaka ne a kan rashin bin umarnin da hukumar ta bayar a baya na iyakance kiyasin lissafin kuɗi ga masu amfani da wutar lantarki.

Hukuncin, wanda aka zayyana a cikin takarda mai suna ‘Order NERC/2024/114’, wani ɓangare ne na umarnin hukumar na watan Satumba na shekarar 2024.

Umurnin mai kwanan watan Agusta 30, ya samu sa hannun mataimakin shugaban NERC Musiliu Oseni da kwamishinan shari’a da lasisi da bin doka, Dafe Akpeneye.

Tarar ta fito ne ta shafin intanet na NERC kamar yadda gidan talabijin na Channels ya ruwaito.

Binciken da NERC ta yi kan tsarin biyan kudi na AEDC ya nuna cewa kamfanin tsalawa kwastomomi fiye da kima a tsakanin watan Janairu zuwa Satumba na 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp