Home General NERC ta ci tarar kamfanin AEDC kan tsauwala kuɗin wuta

NERC ta ci tarar kamfanin AEDC kan tsauwala kuɗin wuta

Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Najeriya (NERC) ta ci kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Abuja (AEDC) tarar Naira Biliyan 1.69 bisa laifin tsauwala wa abokan hulɗarsu kuɗin wuta

Gidan talbijin na Channels ya rawaito cewar tarar ta ta’allaka ne a kan rashin bin umarnin da hukumar ta bayar a baya na iyakance kiyasin lissafin kuɗi ga masu amfani da wutar lantarki.

Hukuncin, wanda aka zayyana a cikin takarda mai suna ‘Order NERC/2024/114’, wani ɓangare ne na umarnin hukumar na watan Satumba na shekarar 2024.

Umurnin mai kwanan watan Agusta 30, ya samu sa hannun mataimakin shugaban NERC Musiliu Oseni da kwamishinan shari’a da lasisi da bin doka, Dafe Akpeneye.

Tarar ta fito ne ta shafin intanet na NERC kamar yadda gidan talabijin na Channels ya ruwaito.

Binciken da NERC ta yi kan tsarin biyan kudi na AEDC ya nuna cewa kamfanin tsalawa kwastomomi fiye da kima a tsakanin watan Janairu zuwa Satumba na 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp