Home General Sojojin Nijeriya sun tarwatsa masarrafar Bom ta ISWAP a jihar Borno

Sojojin Nijeriya sun tarwatsa masarrafar Bom ta ISWAP a jihar Borno

Dakarun sojin Nijeriya sun sami nasarar tarwatsa masarrafar bom mallakin kungiyar tayar da kayar baya ta ISWAP a mashigar Abulam zuwa BUK dake karamar hukumar Damboa a jihar Borno dake Arewa maso gabashin kasar.

Wannan dai na daga cikin kokarin rundunar na kakkabe ayyukan ‘yan ta’adda a yankin tafkin Chadi dake fama matsalar rashin tsaro.

Zagazola makama ya ruwaito cewa dakarun na cigaba da samun nasarar ne tare da bankado ayyukan ‘yan ta’addan bisa hadin gwiwa da dakarun HUBRID da na JTF karkashin Operation Deset Sanity III hadin gwiwa da Operation Hadin Kai wannan yasa suke kara kutsawa maboyar ‘yan ta’addan.

Ayyukan dakarun sojojin dake karkashin kulawar rundunar sojojin saman Nijeriya ya sami gagarumar nasarar inda ya bankado maboyar ‘yan ta’addan dake yankunan Timbuktu da suka hadar da Talala, Gorgi duk dake kusa da dajin Sambisa.

A yayin sumamen sojoji da ‘yan bindigar sun yi musayar wuta inda suka hallaka da dama yayin da wasu kuma suka tsere da raunin harbin bindiga a jikin su, haka kuma a BUK sojojin sun bankado inda ‘yan ta’addan ke sarrafa Bom tare da kwato masu tarin yawa.

Daga nan sojojin sun isa zuwa maboyar kwamandan ‘yan ta’adda Abu Aisha dake Dusula, sai dai kafin su karasa tuni sun gudu don tserewa yin gaba da gaba da sojojin.

Zagazola ya ruwaito cewa sumamen sojojin ya sa sun tarwatsa maboyar kwamandojin mayakan na ISWAP da suka hadar da Hanzala Kaid, Abu Ibrahim, Baa Idrissa, Rawana, Mallam Abubakar da Abu Aisha wanda suka gudu ta yankunan Abba Gajiri da Bulabulin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp