Home General Sojojin Nijeriya sun tarwatsa masarrafar Bom ta ISWAP a jihar Borno

Sojojin Nijeriya sun tarwatsa masarrafar Bom ta ISWAP a jihar Borno

Dakarun sojin Nijeriya sun sami nasarar tarwatsa masarrafar bom mallakin kungiyar tayar da kayar baya ta ISWAP a mashigar Abulam zuwa BUK dake karamar hukumar Damboa a jihar Borno dake Arewa maso gabashin kasar.

Wannan dai na daga cikin kokarin rundunar na kakkabe ayyukan ‘yan ta’adda a yankin tafkin Chadi dake fama matsalar rashin tsaro.

Zagazola makama ya ruwaito cewa dakarun na cigaba da samun nasarar ne tare da bankado ayyukan ‘yan ta’addan bisa hadin gwiwa da dakarun HUBRID da na JTF karkashin Operation Deset Sanity III hadin gwiwa da Operation Hadin Kai wannan yasa suke kara kutsawa maboyar ‘yan ta’addan.

Ayyukan dakarun sojojin dake karkashin kulawar rundunar sojojin saman Nijeriya ya sami gagarumar nasarar inda ya bankado maboyar ‘yan ta’addan dake yankunan Timbuktu da suka hadar da Talala, Gorgi duk dake kusa da dajin Sambisa.

A yayin sumamen sojoji da ‘yan bindigar sun yi musayar wuta inda suka hallaka da dama yayin da wasu kuma suka tsere da raunin harbin bindiga a jikin su, haka kuma a BUK sojojin sun bankado inda ‘yan ta’addan ke sarrafa Bom tare da kwato masu tarin yawa.

Daga nan sojojin sun isa zuwa maboyar kwamandan ‘yan ta’adda Abu Aisha dake Dusula, sai dai kafin su karasa tuni sun gudu don tserewa yin gaba da gaba da sojojin.

Zagazola ya ruwaito cewa sumamen sojojin ya sa sun tarwatsa maboyar kwamandojin mayakan na ISWAP da suka hadar da Hanzala Kaid, Abu Ibrahim, Baa Idrissa, Rawana, Mallam Abubakar da Abu Aisha wanda suka gudu ta yankunan Abba Gajiri da Bulabulin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp