Home General Sojojin Nijeriya sun tarwatsa masarrafar Bom ta ISWAP a jihar Borno

Sojojin Nijeriya sun tarwatsa masarrafar Bom ta ISWAP a jihar Borno

Dakarun sojin Nijeriya sun sami nasarar tarwatsa masarrafar bom mallakin kungiyar tayar da kayar baya ta ISWAP a mashigar Abulam zuwa BUK dake karamar hukumar Damboa a jihar Borno dake Arewa maso gabashin kasar.

Wannan dai na daga cikin kokarin rundunar na kakkabe ayyukan ‘yan ta’adda a yankin tafkin Chadi dake fama matsalar rashin tsaro.

Zagazola makama ya ruwaito cewa dakarun na cigaba da samun nasarar ne tare da bankado ayyukan ‘yan ta’addan bisa hadin gwiwa da dakarun HUBRID da na JTF karkashin Operation Deset Sanity III hadin gwiwa da Operation Hadin Kai wannan yasa suke kara kutsawa maboyar ‘yan ta’addan.

Ayyukan dakarun sojojin dake karkashin kulawar rundunar sojojin saman Nijeriya ya sami gagarumar nasarar inda ya bankado maboyar ‘yan ta’addan dake yankunan Timbuktu da suka hadar da Talala, Gorgi duk dake kusa da dajin Sambisa.

A yayin sumamen sojoji da ‘yan bindigar sun yi musayar wuta inda suka hallaka da dama yayin da wasu kuma suka tsere da raunin harbin bindiga a jikin su, haka kuma a BUK sojojin sun bankado inda ‘yan ta’addan ke sarrafa Bom tare da kwato masu tarin yawa.

Daga nan sojojin sun isa zuwa maboyar kwamandan ‘yan ta’adda Abu Aisha dake Dusula, sai dai kafin su karasa tuni sun gudu don tserewa yin gaba da gaba da sojojin.

Zagazola ya ruwaito cewa sumamen sojojin ya sa sun tarwatsa maboyar kwamandojin mayakan na ISWAP da suka hadar da Hanzala Kaid, Abu Ibrahim, Baa Idrissa, Rawana, Mallam Abubakar da Abu Aisha wanda suka gudu ta yankunan Abba Gajiri da Bulabulin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp