Home General Harin ƙwanton ɓauna yayi sanadiyyar sojoji 3 da ‘yan sanda 7 a...

Harin ƙwanton ɓauna yayi sanadiyyar sojoji 3 da ‘yan sanda 7 a Zamfara

Rundunar ƴan sandan jihar Zamfara ta tabbatar da mutuwar jami’anta 4 da na sojoji 3, a ƙoƙarinsu na daƙile harin da ƴan bindiga suka kai wani kamfanin gine-gine da ke kan babbar hanyar Funtua zuwa Gusau a jihar Zamfara.

Kwamishinan ƴan sandan jihar Mohammed Dalijan ne ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce ƴan bindigar sun yi wa jami’an tsaron kwantan ɓauna ne a lokacin da suka yi yunkurin kai ɗauki wurin da ƴan bindigar suka kai hari.

Sai dai ƙwamishinan ƴan sandan ya tabbatar da cewar jami’an tsaron sun yi kokarin daƙile harin da ƴan bindiga suka kai kamfanin gine-ginen na Setraco.

Lamarin dai ya faru ne a kauyen Ƴandoto da ke yankin ƙaramar hukumar Tsafe na jihar Zamfara, da misalin ƙarfe 9 na safiyar jiya Alhamis.

wannan nan dai shi ne harin na biyu da ƴan bindigar suka kai kan babbar hanyar Funtua zuwa Gusau` cikin ƴan sa’oi, inda suka yi garkuwa da matafiya da dama da ke amfani da hanyar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp