Home General Harin ƙwanton ɓauna yayi sanadiyyar sojoji 3 da ‘yan sanda 7 a...

Harin ƙwanton ɓauna yayi sanadiyyar sojoji 3 da ‘yan sanda 7 a Zamfara

Rundunar ƴan sandan jihar Zamfara ta tabbatar da mutuwar jami’anta 4 da na sojoji 3, a ƙoƙarinsu na daƙile harin da ƴan bindiga suka kai wani kamfanin gine-gine da ke kan babbar hanyar Funtua zuwa Gusau a jihar Zamfara.

Kwamishinan ƴan sandan jihar Mohammed Dalijan ne ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce ƴan bindigar sun yi wa jami’an tsaron kwantan ɓauna ne a lokacin da suka yi yunkurin kai ɗauki wurin da ƴan bindigar suka kai hari.

Sai dai ƙwamishinan ƴan sandan ya tabbatar da cewar jami’an tsaron sun yi kokarin daƙile harin da ƴan bindiga suka kai kamfanin gine-ginen na Setraco.

Lamarin dai ya faru ne a kauyen Ƴandoto da ke yankin ƙaramar hukumar Tsafe na jihar Zamfara, da misalin ƙarfe 9 na safiyar jiya Alhamis.

wannan nan dai shi ne harin na biyu da ƴan bindigar suka kai kan babbar hanyar Funtua zuwa Gusau` cikin ƴan sa’oi, inda suka yi garkuwa da matafiya da dama da ke amfani da hanyar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp