Home AFIRKA Shugaba Faye ya rushe majalisar dokokin Senegal tare da sanya ranar sake...

Shugaba Faye ya rushe majalisar dokokin Senegal tare da sanya ranar sake zaɓe

Shugaban Senegal Bassirou Diomaye Faye ya rushe majalisar dokokin ƙasar da ƴan adawa ke da rinjaye a cikinta, tare da sanar da ranar 17 ga watan Nuwamba don gudanar da zaɓensu.

Faye wanda ya lashe zaɓen ƙasar da aka gudanar a watan Maris na wannan shekarar, tare da faraministansa Ousmane Sonko, sun yi wa ƴan ƙasar alkawarin kawo sauyi mai ma’ana.

To sai dai gwamnatin su na fuskantar koma baya wajen aiwatar da manufofinta, sakamakon rashin rinjayen da su ke da shi a zauren majalisar.

A cewar kundin tsarin mulkin Senegal, Faye na da ikon rushe majalisar dokokin da ke da rinjayen ƴan adawa, tare da sanya ranar da za a gudanar da zaɓensu don samun rinjayen da suke buƙata, wanda hakan kuma zai basu damar aiwatar da kudurorinsu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp