Home General Gwamnatin NIjeriya ta bayar da hutun Ranar Haihuwar Annabi S.A.W

Gwamnatin NIjeriya ta bayar da hutun Ranar Haihuwar Annabi S.A.W

Gwamnatin Najeriya ta ayyana ranar Litinin 16 ga watan Satumba, a matsayin ranar hutu ga ma’aikatan ƙasar, domin bikin ranar Maulidi.

Cikin wata sanarwa da babban sakatare a ma’aikatar cikin gida ta ƙasar, Dr. Magdalene Ajani ya fitar, ya ce ministan ma’aikatar, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hutun a madadin gwamnatin tarayya.

Al’ummar musulmai a faɗin duniya na gudanar da bukukuwan Maulidi domin tunawa da zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammad (S.A.W)

”Gwamnati na taya al’ummar musulman ciki da waɗanda ke zaune a ƙetare murnar zagayowar ranar Maulidin”, in ji sanarwar.

Haka kuma ministan ya yi kira ga musulman ƙasar su yi amfani da lokacin bukukuwan wajen yi wa ƙasar addu’ar zaman lafiya da ci gaban ƙasar.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp