Home General Gwamnatin NIjeriya ta bayar da hutun Ranar Haihuwar Annabi S.A.W

Gwamnatin NIjeriya ta bayar da hutun Ranar Haihuwar Annabi S.A.W

Bola Ahned Tinubu

Gwamnatin Najeriya ta ayyana ranar Litinin 16 ga watan Satumba, a matsayin ranar hutu ga ma’aikatan ƙasar, domin bikin ranar Maulidi.

Cikin wata sanarwa da babban sakatare a ma’aikatar cikin gida ta ƙasar, Dr. Magdalene Ajani ya fitar, ya ce ministan ma’aikatar, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hutun a madadin gwamnatin tarayya.

Al’ummar musulmai a faɗin duniya na gudanar da bukukuwan Maulidi domin tunawa da zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammad (S.A.W)

”Gwamnati na taya al’ummar musulman ciki da waɗanda ke zaune a ƙetare murnar zagayowar ranar Maulidin”, in ji sanarwar.

Haka kuma ministan ya yi kira ga musulman ƙasar su yi amfani da lokacin bukukuwan wajen yi wa ƙasar addu’ar zaman lafiya da ci gaban ƙasar.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp