Home AFIRKA Gwamnatin Sudan ta Kudu na ganawar gaggawa bayan ɗage zaɓe

Gwamnatin Sudan ta Kudu na ganawar gaggawa bayan ɗage zaɓe

Jami’an gwamnatin Sudan ta Kudu na gudanar da ganawar gaggawa sa’o’i bayan sanar da ɗage zaɓen ƙasar zuwa nan da shekara biyu masu zuwa.

A baya an tsara gudanar da zaɓukan cikin watan Disamba mai zuwa.

A shekarar 2018 aka cimma yaryajejeniyar zaman lafiya da ta bai wa shugaban ƙasar, Silva Kiir damar ci gaba da zama shugaban gwamnatin riƙon ƙwarya, yayin da tsohon abokan hamayyarsa, Riek Machar ya zama mataimakinsa.

Ƙasar Sudan ta Kudu ba ta taɓa gudanar da babban zaɓe ba tun bayan ɓallewar ƙasar a 2011.

Matakin jinkirta zaɓen zuwa shekara biyu nan gaba, bai zowa da jama’a da ‘yan ƙasar da mamaki ba.

Shugabannin siyasar ƙasar ba su shirya wa gudanar da zaɓukan a ƙasar ba.

Hakan ne ma ke ƙara haifar da shakkun cewa suna ƙoƙarin tabbatar da kansu a ikon ƙasar mai arzikin man fetur.

Ofishin shugaban ƙasar ya ce ya kamata a gudanar da wasu muhimman abubuwa kamar rubuta sabon kundin tsarin mulkin ƙasar kafin gudanar da zaɓen.

Haka kuma jami’an ƙasar sun bayyana matsalolin tsaro da rashin shiryawa zaɓen a matsayin hujjar ɗage zaɓen.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp