Home AFIRKA Gwamnatin Sudan ta Kudu na ganawar gaggawa bayan ɗage zaɓe

Gwamnatin Sudan ta Kudu na ganawar gaggawa bayan ɗage zaɓe

Jami’an gwamnatin Sudan ta Kudu na gudanar da ganawar gaggawa sa’o’i bayan sanar da ɗage zaɓen ƙasar zuwa nan da shekara biyu masu zuwa.

A baya an tsara gudanar da zaɓukan cikin watan Disamba mai zuwa.

A shekarar 2018 aka cimma yaryajejeniyar zaman lafiya da ta bai wa shugaban ƙasar, Silva Kiir damar ci gaba da zama shugaban gwamnatin riƙon ƙwarya, yayin da tsohon abokan hamayyarsa, Riek Machar ya zama mataimakinsa.

Ƙasar Sudan ta Kudu ba ta taɓa gudanar da babban zaɓe ba tun bayan ɓallewar ƙasar a 2011.

Matakin jinkirta zaɓen zuwa shekara biyu nan gaba, bai zowa da jama’a da ‘yan ƙasar da mamaki ba.

Shugabannin siyasar ƙasar ba su shirya wa gudanar da zaɓukan a ƙasar ba.

Hakan ne ma ke ƙara haifar da shakkun cewa suna ƙoƙarin tabbatar da kansu a ikon ƙasar mai arzikin man fetur.

Ofishin shugaban ƙasar ya ce ya kamata a gudanar da wasu muhimman abubuwa kamar rubuta sabon kundin tsarin mulkin ƙasar kafin gudanar da zaɓen.

Haka kuma jami’an ƙasar sun bayyana matsalolin tsaro da rashin shiryawa zaɓen a matsayin hujjar ɗage zaɓen.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp