Home AFIRKA Gwamnatin Sudan ta Kudu na ganawar gaggawa bayan ɗage zaɓe

Gwamnatin Sudan ta Kudu na ganawar gaggawa bayan ɗage zaɓe

Jami’an gwamnatin Sudan ta Kudu na gudanar da ganawar gaggawa sa’o’i bayan sanar da ɗage zaɓen ƙasar zuwa nan da shekara biyu masu zuwa.

A baya an tsara gudanar da zaɓukan cikin watan Disamba mai zuwa.

A shekarar 2018 aka cimma yaryajejeniyar zaman lafiya da ta bai wa shugaban ƙasar, Silva Kiir damar ci gaba da zama shugaban gwamnatin riƙon ƙwarya, yayin da tsohon abokan hamayyarsa, Riek Machar ya zama mataimakinsa.

Ƙasar Sudan ta Kudu ba ta taɓa gudanar da babban zaɓe ba tun bayan ɓallewar ƙasar a 2011.

Matakin jinkirta zaɓen zuwa shekara biyu nan gaba, bai zowa da jama’a da ‘yan ƙasar da mamaki ba.

Shugabannin siyasar ƙasar ba su shirya wa gudanar da zaɓukan a ƙasar ba.

Hakan ne ma ke ƙara haifar da shakkun cewa suna ƙoƙarin tabbatar da kansu a ikon ƙasar mai arzikin man fetur.

Ofishin shugaban ƙasar ya ce ya kamata a gudanar da wasu muhimman abubuwa kamar rubuta sabon kundin tsarin mulkin ƙasar kafin gudanar da zaɓen.

Haka kuma jami’an ƙasar sun bayyana matsalolin tsaro da rashin shiryawa zaɓen a matsayin hujjar ɗage zaɓen.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp