Home General COAS Lagbaja ya mutu yana da shekaru 56

COAS Lagbaja ya mutu yana da shekaru 56

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya bayyana mutuwar shugaban rundunar sojin Nijeriya Laftanar Janar Taoreed Abiodun Lagbaja, wanda ya mutu yana da shekaru 56 a duniya.

Wannan na cikin wata sanarwa da masawarci na musamman ga shugaban kasar kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga ya fita, aka raba manema labarai a birnin tarayya Abuja.

Jaridar PRNigeria ta ruwaito cewa Taoreed Abiodun Lagbaja ya mutu a daren talata bayan fama da rashin lafiya.

An haifi Taoreed Lagbaja a 28 ga watan Fabrerun 1968, sannan shugaban kasa Asiwajo Bola Ahmad ya nadashi matsayin Hafsan sojojin Najeriya a ranar 19 ga watan Yunin 2023.

ya fara aiki da rundunar sojin kasar ne bayan daukar horo a kwalejin sojojin kasar ta Nigerian Defence Academy a 1987, in da a ranar 19 ga watan satumba 1992, ya fito a matsayin Second Lieutenant rukuni na 39 (39th Regular Course).

a yayin aikinsa Lt. General Lagbaja ya nuna gogewa da shugabanci na gari gami da sadaukar a matsayin kwamandan bataliya ta 72 rukunin sojoji na musamman.

ya kuma taimaka matuka wajen gudanar da ayyukan tsaron cikin gida, wanda ya hadar da jagarantar dakarun OPERATION ZAKI a jihar Benue, Lafiya Dole a jihar Borno, Udoka a kudancin Nijeriya, da Operation Forest Sanity a yankin Jihohin Kaduna da Niger.

haka kuma ya halarci kwalejin sojoji ta Amurka in da ya yi sami digiri na II a dabaru wato “Strategic Studies” wanda hakan ya bashi damar nuna sadaukarwa da kwarewa gami na son cigaban harkokin shugabancia a ayyukan soji.

Lt. General Lagbaja yana da Mata daya Mai suna Mariya da ‘ya’ya guda biyu.

daga bisani shugaba Tinubu ya mika ta’aziyyarsa ga iyalai da rundunar sojin Nijeriya bisa wannan rashi ya kuma yi masa addu’a da kasa baki daya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp