Home General COAS Lagbaja ya mutu yana da shekaru 56

COAS Lagbaja ya mutu yana da shekaru 56

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya bayyana mutuwar shugaban rundunar sojin Nijeriya Laftanar Janar Taoreed Abiodun Lagbaja, wanda ya mutu yana da shekaru 56 a duniya.

Wannan na cikin wata sanarwa da masawarci na musamman ga shugaban kasar kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga ya fita, aka raba manema labarai a birnin tarayya Abuja.

Jaridar PRNigeria ta ruwaito cewa Taoreed Abiodun Lagbaja ya mutu a daren talata bayan fama da rashin lafiya.

An haifi Taoreed Lagbaja a 28 ga watan Fabrerun 1968, sannan shugaban kasa Asiwajo Bola Ahmad ya nadashi matsayin Hafsan sojojin Najeriya a ranar 19 ga watan Yunin 2023.

ya fara aiki da rundunar sojin kasar ne bayan daukar horo a kwalejin sojojin kasar ta Nigerian Defence Academy a 1987, in da a ranar 19 ga watan satumba 1992, ya fito a matsayin Second Lieutenant rukuni na 39 (39th Regular Course).

a yayin aikinsa Lt. General Lagbaja ya nuna gogewa da shugabanci na gari gami da sadaukar a matsayin kwamandan bataliya ta 72 rukunin sojoji na musamman.

ya kuma taimaka matuka wajen gudanar da ayyukan tsaron cikin gida, wanda ya hadar da jagarantar dakarun OPERATION ZAKI a jihar Benue, Lafiya Dole a jihar Borno, Udoka a kudancin Nijeriya, da Operation Forest Sanity a yankin Jihohin Kaduna da Niger.

haka kuma ya halarci kwalejin sojoji ta Amurka in da ya yi sami digiri na II a dabaru wato “Strategic Studies” wanda hakan ya bashi damar nuna sadaukarwa da kwarewa gami na son cigaban harkokin shugabancia a ayyukan soji.

Lt. General Lagbaja yana da Mata daya Mai suna Mariya da ‘ya’ya guda biyu.

daga bisani shugaba Tinubu ya mika ta’aziyyarsa ga iyalai da rundunar sojin Nijeriya bisa wannan rashi ya kuma yi masa addu’a da kasa baki daya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp